< Psalms 29 >
1 You angels in heaven, praise Yahweh! Praise him because he is very glorious and powerful.
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Proclaim that (he/his name) is glorious; bow down before Yahweh in his holy [temple].
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 Yahweh’s voice is heard above the oceans; Yahweh, the glorious God, thunders. His voice thunders over the huge oceans [DOU].
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 His voice is powerful and majestic.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 The sound of Yahweh’s voice breaks great cedar trees, the cedars that grow in Lebanon.
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 He causes [the mountains in] Lebanon to jump like calves jump, and causes Hermon [Mountain] to jump like a young bull jumps.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 Yahweh’s voice causes lightning to flash.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 His voice causes the desert to shake; he shakes Kadesh Desert [in the southern part of Judah].
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 Yahweh’s voice shakes the huge oak trees and strips the leaves from the trees while the people in the temple shout, “Praise [God]!”
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 Yahweh ruled over the flood [that covered the earth]; he is our King who will rule forever.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 Yahweh enables his people to be strong, and he blesses them by causing things to go well for them.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.