< Psalms 24 >

1 The earth and everything in it belongs to Yahweh; all the people in the world belong to him, too,
Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
2 because he caused the ground to be above the water, above the water that was deep below the surface of the earth.
gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
3 Who will be allowed to go up on Zion Hill [in Jerusalem], in order to stand [and worship] in Yahweh’s holy temple?
Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
4 [Only] those whose actions [MTY] and thoughts are pure, who have not worshiped idols, and who do not tell lies when they have solemnly promised [to tell the truth].
Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
5 (They will be blessed by Yahweh/Yahweh will bless them). When God [judges them], he, who has saved them, will say that they (have done nothing wrong/are without fault).
Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
6 They are the ones who approach God, they are the ones who may worship God, the one [we] Israelis worship.
Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
7 Open up [APO] the [temple] gates in order that our glorious king may enter!
Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
8 [Do you know] who the glorious king is? He is Yahweh, the one who is very strong [DOU]; He is Yahweh, who conquers [all his enemies] in battles!
Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
9 Open up the [temple] gates in order that our glorious king may enter!
Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
10 [Do you know] who the glorious king is? He is Yahweh almighty; he is our glorious king!
Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)

< Psalms 24 >