< Psalms 18 >
1 Yahweh, I love you, the one who enables me to be strong.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 Yahweh is like an [overhanging] rock [DOU, MET] [under which I can hide from my enemies]; he is like a strong fortress, the one who protects me; he protects me like a shield [MET] [protects a soldier]; he is the one to whom I go (for refuge/to be protected/safe), and he defends me by his great power [IDM].
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 I called out to Yahweh, who deserves to be praised, and he rescued me from my enemies.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 All around me were dangerous situations in which I might be killed [PRS]; it was as though there were huge waves [MET] that almost crashed on me and killed me.
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 [It was as though] the place where dead people are had ropes that were wrapped around me, or [it was as though] there was a trap [MET] that would [seize and] kill me. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
6 But when I was very distressed, I called out to Yahweh, and from his temple he heard me. He listened to me when I cried out [for help].
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 Then the earth quaked/shook strongly [DOU]; the mountains shook very strongly from their centers [DOU] because Yahweh was angry.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 [It was as though] smoke poured out from his nostrils, and [as though] burning coals came out of his mouth.
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 He opened the sky and came down with a black cloud under his feet.
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 He flew, riding on the back of a creature that had wings, traveling [fast], blown along by the wind.
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 Darkness was all around him [like a blanket] [MET]; dark clouds, full of moisture, covered him [MET].
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 Hailstones and flashes of lightning were around him; hail and burning coals fell from the sky.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 Then Yahweh [spoke in a loud voice] from the sky, and [his enemies] heard his voice that sounded like thunder.
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 He shot his arrows at them and caused them to scatter; His flashes of lightning caused them to become very confused (OR, to run away).
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 The bottom of the ocean became visible, and the foundations of the earth were uncovered, when Yahweh rebuked his enemies when he snorted.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 [It was as though] he reached down from heaven and grabbed me and pulled me up out of the deep ocean.
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 He rescued me from my strong enemies who hated me; they were very strong, with the result that I [could not defeat them].
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 When I (was distressed/had troubles), they attacked me, but Yahweh defended/protected me.
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 He led me to a place where I was safe; he rescued me because he was pleased with me.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 Yahweh has rewarded me because I do what is right; he has blessed me because I (am innocent/have not done things that are wrong).
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 I have obeyed Yahweh’s laws; I have not abandoned him.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 My behavior was directed by his rules; I have not stopped obeying them.
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 He knows that I have not done what is wrong; I have kept myself from sinning.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 So he rewards me because I do what is right; he knows that I [SYN] have not committed sins.
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 Yahweh, you are faithful to those who faithfully [do what you tell them to do]; you always do what is good/right to those who do what you want them to do.
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 You are kind to those who are kind to others, but you act wisely toward those who (act perversely/do bad things).
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 You save those who are humble, but you cause those who are proud to be humiliated/ashamed.
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 You give light to my [soul/spirit]; you take away the darkness of my soul.
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 You enable me to be strong, with the result that I can run and attack a line of enemy soldiers; with your help I can (scale/climb up) the walls [that surround my enemies’ cities].
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 Everything that Yahweh my God does is perfect. We can depend on him to do what he promises. He is like a shield [MET] to protect all those who go to him for refuge.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 Yahweh is [RHQ] the only one who is God; only he is like an [overhanging] rock [under which we can be safe].
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 God is the one who enables me to be strong and who keeps me safe on the roads that I walk on.
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 He enables me to [walk swiftly without stumbling], like a deer walks/runs in the mountains.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 He teaches me how to use a strong/metal bow in order that I can use it to fight in battles.
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 Yahweh, you protect and save me with your shield; you have made me safe by your power [MTY]. I have become (strong/a great [king]) because you have helped me.
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 You have cleared the road for me, with the result that now I do not slip/stumble.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 I have pursued my enemies and caught them; I did not stop until I had defeated/killed them all.
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 When I strike them, they are not able to get up again; they lie on the ground, defeated.
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 You have enabled me to be strong in order that I can fight battles and defeat my enemies.
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 You caused my enemies to run away (OR, you enabled me to put my foot on my enemies’ necks [after I captured them and forced them to lie on the ground]); I have gotten rid of all those who hated me.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 They called out for someone to help them, but no one saved them.
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 I pulverize them, with the result that they become like [MET] the dust that the wind [blows away]; I throw them out like [SIM] [people throw] dirt out into the streets.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 You enabled me to defeat those who fought against me, and appointed me to be the ruler of [many]; people whom I did not know about previously are now slaves [in my kingdom].
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 When foreigners hear about me, they (cringe/bow low before me) and they obey me.
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 They are no longer courageous, and from their forts [where they were hiding] they come [to me] trembling.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 Yahweh is alive! Praise the one who is like an [overhanging] rock [MET] [under which I am safe] Exalt the God who saves me!
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 He enables me to get revenge on my enemies; he causes me to defeat nations and to rule over them,
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 and he rescues me from my enemies. He has lifted me up high so that violent men could not reach me [and harm me].
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 So I praise him [and I tell] the nations [the great things that he has done].
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 He has enabled me, his king, to powerfully defeat my enemies; he faithfully loves me, David, the one he has chosen [to be king], and he will faithfully love my descendants forever.
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.