< Psalms 147 >

1 Praise Yahweh! It is good to sing to praise our God. It is a delightful thing to do and the right thing to do.
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 [Jerusalem was destroyed, but] Yahweh is [enabling us to] build Jerusalem again. He is bringing back the people who were taken [to Babylonia].
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 He enables those who were very discouraged to be encouraged again; [it is as though] they have wounds and he bandages them.
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 He has determined how many stars there will be, and he gives names to all of them.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Yahweh is great and very powerful, and no one can measure how much he understands.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 Yahweh lifts up those who have been oppressed, and he throws the wicked down to the ground.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Thank Yahweh while you are singing to him to praise him; on the harps, play music to our God.
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 He covers the sky with clouds, [and then] he sends rain to the earth and causes grass to grow on the hills.
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 He gives to animals the food that they [need], and gives food to young crows/birds when they cry out [because they are hungry].
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 He is not pleased with strong horses or with men who can run [MTY] fast.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 Instead, what pleases him are those who revere him, those who confidently expect him to continue to faithfully love them.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 [You people of] [APO] Jerusalem, praise Yahweh! Praise your God!
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 He [guards your city] by keeping its gates strong. He blesses the people who live there.
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 He protects the borders [of your country, so that enemies from other countries cannot attack you]. He gives you plenty of very good wheat/grain to eat.
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 He commands what he wants to be done on the earth, and his words quickly come to the place to which he sends them.
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 He sends snow which [covers the ground] like a white wool blanket [SIM], and he scatters frost [on the ground] like [wind scatters] ashes [SIM].
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 He sends hail down like (pebbles/tiny stones); [when that happens], (it is very difficult to endure because the air becomes very cold./who can endure because the air becomes very cold?) [RHQ]
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 [But] he commands the wind to blow, and it blows. [Then the hail] melts and [the water] flows [into the streams].
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 He sent his message to [the descendants of] Jacob; [he tells to his] Israeli people the laws and regulations that he had decreed.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 He has not done that for any other nation; the other nations do not know his laws. Praise Yahweh!
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.

< Psalms 147 >