< Psalms 14 >

1 [Only] foolish people say to themselves, “There is no God!” People who say those things are corrupt/worthless; they do abominable/detestable deeds; there is not one [of them] who does what is good/right.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
2 Yahweh looks down from heaven and sees humans; he looks to see if anyone is very wise, with the result that he desires [to know] God.
Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
3 But they are all corrupt/evil; no one does what is good/right.
Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
4 Will those evil people never learn [what God will do to punish them] [RHQ]? They act violently toward Yahweh’s people while eating the food that he provides, and they never pray to Yahweh.
Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
5 But [some day] they will become very terrified because God helps those who act righteously [and will punish those who reject him].
Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
6 Those who do evil may prevent helpless people from doing what they plan to do, but Yahweh protects those helpless people [MET].
Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
7 I wish/desire that [Yahweh] would come from Jerusalem [MTY] and rescue [us] Israeli people! Yahweh, when you bless your people again, all of us Israeli people, who are the descendants of Jacob, will rejoice.
Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!

< Psalms 14 >