< Psalms 139 >
1 Yahweh, you have examined me, and you know [everything about] me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
2 You know when I sit down and when I stand up. [Even though you are] far away from me, you know what I am thinking.
Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
3 When I travel and when I lie down, you know everything that I do.
Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
4 Yahweh, even before I say [MTY] anything, you know everything that I am going to say!
Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
5 You protect me on all sides; you put your hand on me [to protect me with your power] [MTY].
Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
6 I am not able to understand that you know [everything about me]. That is too great for me to really understand.
Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
7 (Where could I go to escape from your Spirit?/I could not go anywhere to escape from your Spirit.) [RHQ] (Where could I go to get away from you?/I could not go anywhere to get away from you.) [RHQ]
Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
8 If I went up to heaven, you would be there. If I lay down in the place where the dead people are, you would be there. (Sheol )
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol )
9 If I had wings and flew very far east [MTY], or if I flew west and made a place to live [on an island] in the ocean,
In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
10 you would be there also, to lead me by your hand, and you would help me.
can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
11 I could request the darkness to hide me, or I could request the light around me to become darkness,
In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
12 but even [if that happened], the darkness would not be darkness for you! For you, the night is [as bright] as the daytime is, because for you, daylight and darkness are (not different/the same).
duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
13 You created [all] the parts of my body; you put [the parts of] my body together when I was still in my mother’s womb.
Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
14 I praise you because you made my [body in a very] awesome and wonderful way. Everything that you do is amazing! I know that very well.
Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
15 When my body was being formed, while it was being put together where no one else could see it, you saw it!
Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
16 You saw me before I was born. You wrote in your book the number of days that you had decided that I would live. You did that before any of those days had [even] started!
Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
17 God, what you think about me is very precious (OR, is very hard to understand). There is a great number of things that you think about.
Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
18 If I could count them, [I would see that] they are more than the grains of sand [at the seashore]. And when I wake up, I am still with you [and I know that there are still more of your thoughts about me to count].
A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
19 God, I desire that you would kill all the wicked people! And I wish that violent [MTY] men would (leave/go away from) me.
Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
20 They say wicked/malicious things about you; they slander your name.
Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
21 Yahweh, I certainly [RHQ] hate those who hate you! And I despise [RHQ] those who rebel against you.
Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
22 I hate them completely, and I consider that they are my enemies.
Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
23 God, search my inner being; find out what I am thinking!
Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
24 Find out whether there is anything evil in my [inner being], and lead me along the road [that leads to my being with you] forever.
Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.