< Psalms 135 >

1 Praise Yahweh! You who (do work for/serve) Yahweh, praise him!
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 You who stand in the temple of Yahweh our God and in the surrounding courtyard, praise him [MTY]!
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Praise Yahweh, because he does good things [for us]; sing to him [MTY], because he is kind [to us].
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 He has chosen [us, the descendants of] Jacob; he has chosen [us] Israelis to belong to him [DOU].
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 I know that Yahweh is great; he is greater than all the gods.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 Yahweh does whatever he desires to do, in heaven and on the earth and in the seas/oceans, [down] to the bottom of the seas.
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 He is the one who causes clouds to appear from very distant places on the earth; he sends lightning with the rain, and he brings the winds from the places where he stores them.
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 He is the one who killed [all] the firstborn [males] in Egypt, the firstborn of people and of animals.
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 There he performed many kinds of miracles [DOU] to punish the king and all his officials.
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 He destroyed many nations and the powerful kings [who ruled them]:
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 Sihon, the king of the Amor people-group, and Og, the king of Bashan [region], and all the other kings in Canaan [land].
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 Then he gave their land to [us] Israeli people to belong to us [forever].
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 Yahweh your name will endure forever, and people who are not yet born will remember the great things [that you have done].
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 Yahweh, [you] declare that we your people (are innocent/have not done things that are wrong), and you are merciful to us.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 But the idols that the [other] people-groups [worship] are only [statues made of] silver and gold, things that humans have made.
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 Their idols have mouths, but they cannot say [anything]; they have eyes, but they cannot see [anything].
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 They have ears, but they cannot hear [anything], and they are not [even able to] breathe.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 The people who make those idols are as [powerless as] those idols, and those who trust in those idols [can accomplish no more than] their idols can!
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 [My fellow] Israelis, praise Yahweh! You [priests] who are descended from Aaron, praise Yahweh!
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 You [men] who are descended from Levi, [you who assist the priests], praise Yahweh! [All] you who revere Yahweh, praise him!
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Praise Yahweh in [the temple on] Zion [Hill] in Jerusalem, where he lives! Praise Yahweh!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Psalms 135 >