< Psalms 11 >

1 I trust that Yahweh will protect [MTY] me. So do not [RHQ] say to me, “You need to escape/flee to the mountains like birds do,
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
2 because wicked people have hidden in the darkness, they have pulled back their bowstrings and aimed their arrows to shoot them at godly/righteous [IDM] people [like you].
Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
3 When people are not punished for disobeying the laws, (what can righteous people do?/there is not much that righteous people can do.)” [RHQ]
Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
4 But Yahweh is sitting on his throne in his sacred temple in heaven, and he [SYN] watches everything that people do.
Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
5 Yahweh examines what righteous people do and what wicked people do, and he hates those who like to perform violent actions [to injure others].
Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
6 He will send down [from the sky] flaming coals and burning sulfur, and send scorching hot winds to punish wicked people.
A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
7 Yahweh is righteous and he loves those who act righteously; righteous people are able to come into his presence.
Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.

< Psalms 11 >