< Obadiah 1 >

1 This is a message that Yahweh our God gave to me, Obadiah, about the Edom [people-group]. Yahweh our God has told me this about [the people of] Edom: “I, Yahweh, have sent a messenger to other nations, telling them to prepare to go and attack Edom.”
Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
2 And Yahweh says this to the people of Edom: “I will soon cause you to become the weakest and most despised nation [on the earth].
“Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
3 Your [capital city] is high in the rocky cliffs, and you are very proud; you think that you are safe from being attacked by your enemies [RHQ], but you [IDM] have deceived yourselves.
Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
4 And I tell you that even if [you had wings and] could fly higher than eagles fly, and if you could make your homes among the stars, I would bring you [crashing] down from there.
Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
5 When thieves break into someone’s house during the night, they certainly [RHQ] steal only the things that they want. And people who pick grapes always [RHQ] leave a few grapes on the vines. But your country will be completely destroyed!
“In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
6 Everything that is valuable will be taken away. [Your enemies] will find and take away even the valuable things that you have hidden.
Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
7 All (your allies/nations who promised to help you) will turn against you, and they will force you to leave your country/land. Those with whom you have peace now will trick/deceive you and defeat you. Those who eat meals with you now are planning to trap you, and [then they will say to you], ‘You are not [RHQ] as clever [as you thought you were]!’
Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
8 I, Yahweh, declare that at the time that I destroy Edom, I will punish the men who live in those cliffs who [thought that they] were wise.
“A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
9 The soldiers from Teman [town] will become terrified; all you people who are descendants of Esau will be (wiped out/killed).
Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
10 You acted cruel in a cruel way toward your relatives who are descendants of Jacob, [the twin brother of your ancestor Esau]. So now you will be disgraced forever; you will be completely destroyed.
Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
11 Foreigners entered the gates of Jerusalem and (cast lots/threw small stones that were marked) to decide what valuable things they would take away; but you were as bad as those foreigners, because you just stood there [and did not help the Israelis].
A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
12 You should not have (gloated/been happy) about the disaster that the Israelis were experiencing. You should not have been happy when their towns were ruined. You should not have made fun [of them] when they were suffering.
Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
13 They are my people, so you should not have entered their [city] gates when they were experiencing those disasters and you should not have laughed at them. And you should not have taken away their [valuable] possessions.
Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
14 You should not have stood at crossroads to catch those who were [trying to] escape. You should not have [captured them and] put them into the hands of [their enemies] when they were experiencing those disasters.”
Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
15 “There will soon be the time when I, Yahweh, will judge [and punish] all the nations. And you [people of Edom] will experience the same [disasters] that you caused [others to experience]. The same evil things that you have done to others will happen to you.
“Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
16 [My people in Jerusalem have been punished] because I was very angry with them. [It is as though] [MET] they drank [a cup of very bitter liquid] on Zion, my sacred hill. But [I] will punish [MET] all the other nations even more severely, and cause them to disappear completely.
Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
17 But some [people in Jerusalem will escape], and Jerusalem will become a very holy/sacred place. Then the descendants of Jacob will [conquer and] possess again the land that truly belongs to them.
Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
18 The descendants [MTY] of Jacob and his son Joseph will be like [MET] a fire, and the people [MTY] of Edom will be like [MET] stubble that will be completely burned in that fire. Not one person will remain alive. [That will surely happen because] I, Yahweh, have said it.”
Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
19 The Israeli people [who live] in the southern desert are the ones who will capture Edom. And those [who live in] the western foothills will capture the Phoenicia [region] and the areas of Ephraim and Samaria. And people of the tribe of Benjamin will conquer the Gilead [region].
Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
20 Those who were (exiled in/forced to go to) [Babylon] will [return to their land] [and] capture the Phoenicia [region] as far north as Zarephath [on the coast of the Mediterranean Sea]. People of Jerusalem who were captured and taken to Sardis, [the capital city of the Lydia region], will capture the towns in the southern desert.
Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
21 The army of Jerusalem will attack Edom and conquer it, and Yahweh will be their king.
Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.

< Obadiah 1 >