< Numbers 5 >

1 Yahweh said to Moses/me,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Tell this to the Israeli people: ‘You must send away from your (camp/area where you have your tents) any man or woman who has leprosy and anyone who has a discharge [of some fluid from his body], and anyone who has become unacceptable to God because of [having touched] a corpse.
“Ka umarci Isra’ilawa su kori duk wanda yake da ciwon fatan jiki, ko mai ɗiga na kowane iri, ko wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, daga cikin sansani.
3 Send them away from there in order that they will not [touch people in the camp area] where I live among you and cause them to become unacceptable to me.’”
Ka kori maza da mata ma; ka kai su bayan sansani domin kada su ƙazantar da sansani inda nake zama a cikinsu.”
4 So [Moses/I told that to the Israeli people, and] the Israeli people obeyed what Yahweh commanded Moses/me.
Isra’ilawa suka yi haka; suka kore su daga sansanin. Suka aikata yadda dai Ubangiji ya umarci Musa.
5 Yahweh also told Moses/me,
Ubangiji ya ce wa Musa,
6 “Tell this to the Israeli people: ‘If someone (commits a crime against/does something wrong to) another person, [I consider that] that person has done wrong to me.
“Gaya wa Isra’ilawa, ‘Sa’ad da namiji ko mace ya yi wa ɗan’uwansa laifi ta kowace hanya, ta yin haka, ya yi rashin aminci ga Ubangiji, mutumin kuwa ya yi laifi ke nan
7 That person must confess that he or she is guilty, and he or she must pay to the person to whom wrong was done [what others consider to be a suitable/proper payment] for what he has done, and he must pay an extra 20 percent.
kuma dole yă furta zunubin da ya yi. Dole yă yi biya cikakkiyar diyya saboda laifinsa, yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar a kai, yă kuma bayar da shi duka ga wanda ya yi wa laifin.
8 If the person against whom the wrong was done [has died and] there is no relative to whom the money can be paid, then the money belongs to me, and it must be paid to the priest. In addition, the one who did the wrong must give a male sheep to the priest [to sacrifice] in order that (that person’s sin may be forgiven/I can forgive that person for his sin).
Amma in mutumin da aka yi wa laifin ba shi da ɗan’uwa na kusa da za a biya diyya saboda laifin, sai diyyar tă zama ta Ubangiji, dole kuma a ba wa firist, haɗe da ragon da za a yi kafara da shi.
9 All the sacred offerings that the Israelis bring to the priest belong to the priest.
Dukan tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka kawo wa firist za su zama nasa.
10 The priest can keep those gifts.’”
Kowace tsarkakakkiyar kyauta da mutum ya kawo nasa ne, sai dai abin da ya ba wa firist, zai zama na firist.’”
11 Yahweh also said this to Moses/me:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
12 “Tell this to the Israeli people: ‘Suppose a man thinks that his wife has slept with another man,
“Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘In matar wani ta kauce, ta kuma yi rashin aminci gare shi
13 but neither he nor anyone else knows if it is true or not, because no one saw her doing that.
ta wurin kwana da wani dabam, wannan kuwa ya kasance a ɓoye ga mijinta, rashin tsarkinta kuwa bai tonu ba (da yake babu shaida, ba a kuma kama ta tana yi ba),
14 But if the woman’s husband is jealous, and if he suspects that she has committed adultery, and he wants to know whether that is true or not,
in kuma kishi ya sha kan mijinta kuma tana da ƙazanta, ko kuwa idan yana kishi yana kuma zatonta ko ma ba ta da ƙazanta
15 he should take his wife to the priest. He must take along as an offering two quarts/liters of barley flour. The priest must not pour [olive] oil or incense on it, because this is an offering that the man has brought because he (is jealous/wants his wife to sleep only with him). It is an offering to find out if she is guilty or not. [Neither olive oil nor incense should be used because are associated with joy and this is not a time for joy.]
mijin zai kai matansa a gaban firist, yă kuma kawo hadayar abubuwan da ake bukata; abubuwa kamar, garin sha’ir garwa ɗaya, amma kada yă zuba mai a kan garin sha’ir, kada kuma yă sa turaren wuta a kansa, domin hadaya ce ta miji mai tuhumar matarsa da aka kawo domin gaskiya tă fito fili.
16 The priest must tell the woman to stand [in front of the altar] in my presence.
“‘Firist zai kawo ta, yă sa tă tsaya a gaban Ubangiji.
17 He must put some sacred water in a clay jar, and then he must put some dirt from the floor of the Sacred Tent into the water.
Sa’an nan zai ɗebi ruwa mai tsarki a tulun laka, yă zuba ƙurar da ya ɗebo daga daɓen tabanakul a cikin ruwan.
18 He must untie/unfasten the woman’s hair. Then he must put in her hands the grain that her jealous husband is offering to determine whether she has committed adultery or not. The priest must hold [the bowl that contains] bitter water that will cause (the woman to be cursed/bad things to happen to the woman) [if she is guilty].
Bayan da firist ya sa matan ta tsaya a gaban Ubangiji, sai yă kunce gashin kanta, yă kuma sa hadaya ta gari don tunawa a hannuwanta, hadayar gari ce ta kishi, yayinda shi kansa zai riƙe ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana.
19 The priest must require her to solemnly declare [that she will tell the truth]. Then he must say to her, “Has another man had sex [EUP] with you? Have you faithfully [slept only with your husband] or not? If you have not slept with another man, nothing bad will happen to you if you drink the water.
Sa’an nan firist zai sa tă yi rantsuwa, yă kuma ce mata, “In ba wani mutumin da ya kwana da ke kuma ba ki kauce kin ƙazantar da kanki yayinda kike auren mijinki ba, kada wannan ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana, yă cuce ki.
20 But if you have had sex with another man, [Yahweh will curse you].
Amma in kin kauce yayinda kike auren mijinki, kika kuma ƙazantar da kanki ta wurin kwana da wani dabam da ba mijinki ba,”
21 Your womb will shrivel up and your stomach will swell up. You will never be able to give birth to children, and as a result, everyone will curse you and avoid you. If you have committed adultery, [when you drink] this water, that is what will happen to you.” Then the woman must answer, “[If I am guilty], I will not object if that happens.”
(a nan firist zai sa macen a ƙarƙashin la’anar rantsuwa cewa) “bari Ubangiji yă sa mutanenki su la’ance ki, su kuma yi Allah wadai da ke, sa’ad da Ubangiji ya sa cinyarki ta shanye, cikinki kuma ya kumbura.
Bari wannan ruwa mai jawo la’ana, yă shiga jikinki saboda cikinki yă kumbura, cinyarki kuma yă shanye.” “‘Sai macen tă ce, “Amin. Bari yă zama haka.”
23 ‘Then the priest must write [with ink] on a small scroll these (curses/bad things that will happen to her if she is guilty) [and then wash the ink off into the bitter water].
“‘Firist zai rubuta waɗannan la’anoni a littafi, sa’an nan yă wanke su cikin ruwa mai ɗaci.
24 The priest must take from her the offering of barley flour [that she is holding], and lift it up to dedicate it to me. Then he must put it on the altar
Sai yă sa macen tă sha ruwa mai ɗaci, mai jawo la’ana, wannan ruwa kuwa zai shiga cikinta yă kawo mata wahala mai zafi.
Firist zai karɓi hadaya ta gari don kishi daga hannuwanta, yă kaɗa shi a gaban Ubangiji sa’an nan yă kawo a bagade.
26 and burn part of it as a sacrifice. Then the woman must drink the bitter water.
Sa’an nan firist zai ɗiba hatsi na hadaya cike da hannunsa don hadayar tunawa, yă kuma ƙone a bagade; bayan haka sai yă sa macen tă sha ruwan.
27 If the woman has committed adultery, the water will cause her to suffer greatly. Her stomach will swell up and her womb will shrink, [and she will be unable to give birth to children]. And then her (relatives/fellow Israelis) will curse her.
In ta ƙazantar da kanta ta kuma ci amanar mijinta, to, yayinda aka sa tă sha ruwa mai jawo la’ana, ruwan zai shiga cikinta, yă jawo mata wahala mai zafi; cikinta zai kumbura, cinyarta kuma yă shanye, tă kuwa zama la’ananniya a cikin mutanenta.
28 But if she (is innocent/has not committed adultery), her body will not be harmed, and she will still be able to give birth to children.
Amma fa, in macen ba tă ƙazantar da kanta ba, ba tă kuma da ƙazanta, za a kuɓutar da ita daga laifin, za tă kuma iya haihuwa.
29 ‘That is the ritual that must be performed when a woman who is married has been unfaithful to her husband,
“‘Wannan dai, ita ce dokar kishi sa’ad da mace ta kauce, ta kuma ƙazantar da kanta yayinda take aure da mijinta,
30 or when a man is jealous and suspects that his wife [has had sex with another man]. The priest must tell that woman to stand [at the altar] in my presence and obey these instructions.
ko kuma sa’ad da mijin yana kishi domin yana shakkar matarsa. Firist zai sa tă tsaya a gaban Ubangiji, yă kuma yi amfani da wannan doka gaba ɗaya a kanta.
31 Even if the woman has not done what the husband suspected, he will not be punished [MTY] for doing something wrong [by bringing his wife to the priest]. But if his wife is guilty, she will suffer as a result.’”
Mijin zai zama marar laifi daga kowane laifi, amma matar za tă ɗauki muguntarta, idan ta yi laifin.’”

< Numbers 5 >