< Numbers 32 >

1 The people of the tribes of Reuben and Gad had much livestock. They saw that the land near Jazer [city] and the Gilead [region east of the Jordan River] had good [grass] for the animals [to graze on].
Mutanen Ruben da mutanen Gad, da suke da garken shanu da kuma garke tumaki masu yawa, suka ga cewa ƙasashen Yazer da Gileyad wurare ne masu kyau don kiwon shanu da tumaki.
2 So their leaders came to Eleazar and the other leaders of the people and Moses/me. They said,
Saboda haka suka zo wurin Musa da Eleyazar da kuma shugabannin jama’a, suka ce,
3 “We have a great amount of livestock.
“Atarot, Dibon, Yazer, Nimra, Heshbon, Eleyale, Sebam, Nebo da Beyon,
4 Yahweh has enabled us Israelis to capture some land that is very good for animals [to graze on]—the land near Ataroth, Dibon, Jazer, Nimrah, Heshbon, Elealeh, Sebam, Nebo, and Beon [towns].
ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban mutane Isra’ila, suna da kyau don dabbobi, bayinku kuma suna da dabbobi.”
5 If it pleases you, we would like this land to be ours, instead of land on the other side of the Jordan River.”
Suka ce, “In mun sami tagomashi daga gare ka bari a ba da wannan ƙasa ga bayinka, tă zama mallakanmu. Kada ka sa mu haye Urdun.”
6 Moses/I replied to the leaders of the tribes of Gad and Reuben, “It is not right for [RHQ] your fellow Israelis to go to fight in wars and you stay here!
Musa ya ce wa mutanen Gad da mutanen Ruben, “Wato, sai’yan’uwanku su yi ta yaƙi ku kuwa ku zauna nan?
7 [If you do that], you will cause the other Israelis to be discouraged, with the result that they will not cross [the Jordan River] to the land that Yahweh is giving to them [RHQ].
Don me za ku karya zuciya Isra’ilawa daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?
8 Your ancestors did the same kind of thing. I sent them from Kadesh-Barnea to see what the land [of Canaan] was like.
Haka iyayenku suka yi sa’ad da na aike su daga Kadesh Barneya don su dubo ƙasar.
9 They went as far as Eshcol Valley, but when they saw [the huge people in] the land, [they returned and] caused the Israeli people to be discouraged, saying ‘We should not try to enter the land that Yahweh said that he is giving to us.’
Gama bayan suka haura Kwarin Eshkol suka hangi ƙasar, sai suka karya zuciyar Isra’ilawa daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su.
10 So Yahweh became very angry with them, and he solemnly declared this:
A ranar kuwa Ubangiji ya husata har ya yi wannan rantsuwa cewa,
11 ‘From all the people who came out of Egypt, the only ones who are at least 20 years old who will see the land that I promised to give to Abraham, Isaac, and Jacob, are Jephunneh’s son Caleb and Nun’s son Joshua, because they trusted me completely. None of the other people who came out of Egypt will even see that land, because they have not completely believed in my [power].’
‘Tabbatacce ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, domin ba su bi ni sosai ba,
ba ko ɗaya sai dai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze da Yoshuwa ɗan Nun, don su ne kaɗai suka bi Ubangiji da zuciya ɗaya.’
13 So Yahweh was angry with the Israeli people, and [as a result] he has caused us to wander in this desert for 40 years. Finally, all the people who had sinned against Yahweh [by refusing to trust him] died, [one by one].
Ubangiji ya husata da Isra’ila har ya sa suka yi ta yawo a hamada shekara arba’in, sai da dukan tsaran da suka aikata wannan mugunta a gabansa, suka mutu.
14 And you are acting like your ancestors did! You sinful Israeli people are going to cause Yahweh to be more angry with you [than he was with our ancestors]
“Ga shi ku kuma, tarin masu zunubi, kuna tsaya a matsayin kakanninku, kuna sa Ubangiji yă sāke husata da Isra’ila.
15 If you stop trusting him, he will cause you and all your fellow Israelis to stay longer in the desert, and he will get rid of all of you!”
In kun juye daga binsa, zai sāke barin dukan wannan mutane a hamada, ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakarsu.”
16 Then the [leaders of the tribes of Reuben and Gad] said to Moses/me, “First we will build pens for our animals and build cities for our families here.
Sai suka zo wurin Musa, suka ce, “Muna so mu gina katangar dutse don dabbobinmu, da kuma birane don matanmu da’ya’yanmu a nan.
17 Then our families will live in strong cities with walls around them, and they will be safe from the people who live in this land. Then we will get ready to fight battles. We will help the other Israelis to get land [on the other side of the river].
Matanmu da’ya’yanmu za su zauna a biranen da suke da katanga, don kāriya daga mazaunan ƙasar, amma mu, za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra’ilawa, har mu kai su wuraren zamansu.
18 We will not return to our homes until every Israeli has received some land.
Ba za mu koma gidajenmu ba sai kowane mutumin Isra’ila ya sami gādonsa.
19 We will not take any land on the west side of the Jordan [River]; our land will be here on the east side.”
Ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayin gabashin Urdun.”
20 So Moses/I told them, “[Okay, I will tell you] what you all must do. You must get ready to fight battles for Yahweh.
Sai Musa ya ce musu, “In za ku yi haka, in za ku sha ɗamara da makamai a gaban Ubangiji, ku tafi yaƙi,
21 You all must cross the Jordan [River] carrying your weapons.
in kuma dukanku za ku yi ɗamara, ku ɗauki makaman yaƙi a hayin Urdun a gaban Ubangiji har lokacin da ya kori abokan gābansa daga gabansa,
22 After Yahweh helps us to take that land [from the people who live there], you will be permitted to return to your homes. You will have done what you have promised Yahweh and the Israeli people that you would do, and you may keep this land to be your own, given to you by Yahweh.
to, sa’ad da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji, kwa kuɓuta daga alhakinku ga Ubangiji da kuma Isra’ila. Ƙasan nan kuwa za tă zama mallakarku a gaban Ubangiji.
23 “But if you do not do these things, you will be sinning against Yahweh, and he will punish you for [that] sin.
“Amma in ba ku yi haka ba, kun yi zunubi ke nan ga Ubangiji; kuma ku san cewa zunubinku zai tone ku.
24 Now you can build cities for your families and pens for your animals, but after doing that, you must do what you have promised.”
Ku gina birane domin matanku da’ya’yanku, ku gina katanga kuma domin dabbobinku, amma fa ku cika abin da kuka yi alkawari.”
25 The leaders of the tribes of Gad and Reuben replied, “We will do what you have asked us to do [MTY], because you are our leader.
Mutanen Gad da mutanen Ruben, suka ce wa Musa, “Mu bayinka za mu yi yadda ranka yă daɗe ya umarta.
26 Our wives and children and our cattle and sheep and goats will stay here in the cities in the Gilead area,
’Ya’yanmu da matanmu, garkunan shanunmu da na tumakinmu, za su kasance a nan biranen Gileyad.
27 but we will prepare to go to battle. We will take our weapons and go across [the Jordan River] and fight for Yahweh, just as you, our leader, have said.”
Amma bayinka, kowane mutum a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji, zuwa yaƙi kamar yadda ranka yă daɗe ya faɗa.”
28 So Moses/I gave instructions about them to Eleazar, Joshua, and the leaders of the Israeli tribes.
Sai Musa ya yi wa Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra’ila kashedi a kansu,
29 Moses/I said to them, “If the men from the tribes of Gad and Reuben prepare for battle and cross the Jordan [River] with you, in order to do what Yahweh desires and help you to take that land, give them the Gilead area to belong to them.
ya ce, “In kowane sojan mutanen Gad da na mutanen Ruben, ya ɗauki makaman yaƙi, ya haye Urdun tare da ku a gaban Ubangiji, to, sa’ad da a ci ƙasar a gabanku, ku ba da ƙasar Gileyad tă zama mallakarsu.
30 But if they do not take their weapons and go with you prepared to fight, they will not receive this land. They will need to accept some land in Canaan, like the rest of you will do.”
Amma in ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo a wancan haye kamar sauran kabilun a Kan’ana.”
31 The [leaders of the tribes of Gad and Reuben] replied, “We will do what you have said and what Yahweh has said.
Mutanen Gad da mutanen Ruben suka amsa, suka ce, “Barorinka za su yi abin da Ubangiji ya faɗa.
32 We will cross the river into Canaan land, and we will do what Yahweh desires and be prepared for battle. But our land will be [here] on the east side of the Jordan [River].”
Za mu haye a gaban Ubangiji zuwa Kan’ana, amma mallakarmu ta gādo, za tă kasance a wannan hayi na Urdun.”
33 So Moses/I agreed to give that land to the tribes of Gad and Reuben and to half of the tribe of Joseph’s son Manasseh. That land was previously the land where Sihon, the king of the Amor people-group, ruled, and the land where Og, the king of Bashan [region], ruled, including its cities and surrounding land.
Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
34 The people of the tribe of Gad rebuilt Dibon, Ataroth, Aroer,
Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
35 Atroth-Shophan, Jazer, Jogbehah,
Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
36 Beth-Nimrah, and Beth-Haran cities. Those were cities with strong walls around them. And they also built pens for their sheep.
Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
37 The people of the tribe of Reuben rebuilt Heshbon, Elealeh, Kiriathaim,
Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
38 Nebo, Baal-Meon, and Sibmah cities. When they rebuilt Nebo and Baal-Meon, they gave new names to those cities.
haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
39 The descendants of Manasseh’s son Makir went to the Gilead [region] and compelled the people of the Amor people-group to leave that area.
Zuriyar Makir ɗan Manasse suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori mutanen Amoriyawa da suke can.
40 So Moses/I gave Gilead to the family of Makir, and they started to live there.
Saboda haka Musa ya ba da Gileyad ga mutanen Makir, zuriyar Manasse, suka kuma zauna a can.
41 Jair, who was also a descendant of Manasseh, went and captured the small towns in that region, and he named them the Towns of Jair.
Yayir, wani ɗan Manasse, ya ci ƙauyukansu da yaƙi, ya kuma ba su sunan Hawwot Yayir.
42 A man named Nobah went and captured Kenath [city] and the nearby towns, and then he put his own name to be the new name of that area.
Noba kuma ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya kuma ba ta suna Noba, bisa ga sunansa.

< Numbers 32 >