< Numbers 30 >

1 Moses/I spoke with the leaders of the Israeli tribes. He/I told them these commands that Yahweh had given to him/me:
Musa ya ce wa shugabannin kabilan Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya umarta.
2 “If a man solemnly promises Yahweh that he will do something, he must do what he promised.
Sa’ad da mutum ya yi wa Ubangiji alkawari, ko kuwa ya rantse zai yi wani abu, kada yă ƙi cika maganarsa, amma yă cika kome da ya faɗa.
3 “If a young woman who is still living with her parents solemnly promises to Yahweh to do something,
“Sa’ad da yarinya, wadda har yanzu tana a gidan mahaifinta ta yi wa Ubangiji alkawari, ko ta rantse za tă yi wani abu,
4 and if her father hears about what she promised, and if he does not object, she must do what she promised [DOU].
mahaifinta kuwa ya ji alkawarin da ta yi, bai kuma ce mata kome ba, to, sai alkawarin da ta yi da wa’adinta su tabbata.
5 But if her father hears about what she promised and does not allow her to do that, then she does not need to do what she promised. Yahweh will forgive her for not doing what she promised.
Amma in mahaifinta ya hana ta, sa’ad da ya ji game da shi, to, ba wani daga cikin alkawari ko rantsuwar da ta yi zai tabbata; Ubangiji kuwa zai gafarta mata domin maihaifinta ya hana ta.
6 “If a woman promises Yahweh that she will do something, but then she gets married,
“In ta yi aure, sai daga baya ta yi alkawari ko kuwa leɓunanta sun furta alkawari da garaje, cewa za tă yi wani abu,
7 if her husband hears about what she promised to do, and he does not object, she must do what she promised [DOU].
mijinta kuwa ya ji game da wannan, amma bai ce mata kome ba, to, alkawarin da ta yi da kuma rantsuwar da ta yi, su tabbata.
8 But if her husband hears about it and does not allow her to do that, she does not need to do what she promised, and Yahweh will forgive her for not doing what she promised.
Amma in mijin ya hana ta sa’ad da ya ji, zai warware alkawari da kuma rantsuwar da ta yi da garaje, Ubangiji kuwa zai gafarce ta.
9 “If a widow or a woman who has been divorced makes a promise, she must do what she promised.
“Duk wani alkawari ko rantsuwar da gwauruwa, ko macen da aurenta ya mutu, ta yi, zai tabbata a kanta.
10 “If a woman who is married promises [DOU] to do something,
“In macen aure ta yi alkawari, ko ta rantse za tă yi wani abu,
11 and if her husband hears about it but does not object, she must do what she promised.
mijinta kuwa ya ji game da wannan, amma bai ce mata kome ba, bai kuma hana ta ba, to, dukan alkawari da kuma rantsuwar da ta yi su tabbata a kanta.
12 But if he hears about it and does not allow her to do that, she does not need to do what she promised, and Yahweh will forgive her for not doing it.
Amma in mijin ya warware su sa’ad da ya ji, to, ba wani alkawari ko rantsuwar da ya fito daga leɓunanta da zai tabbata. Mijinta ya warware su, Ubangiji kuma zai gafarce ta.
13 A woman’s husband may require her to do what she has promised, or he may not allow her to do what she has promised.
Mijinta yana iya tabbatar, ko yă rushe duk wani alkawari ko rantsuwar da ta ɗauka.
14 If he does not object for several days [after he hears about it], she must do what she promised.
Amma in mijinta bai ce mata kome ba, to, ya tabbatar da dukan alkawarinta da kuma rantsuwarta ke nan. Ya tabbatar da su ta wurin yin shiru sa’ad da ya ji ta.
15 But if he waits a long time after she has promised to do something and then he tells her that he will not permit her to do it, if she does not do what she promised, [she will not be punished]; her husband is the one whom [Yahweh] will punish.”
Amma in ya ji, sa’an nan daga baya ya hana ta, to, zai sha hukuncin laifinta.”
16 Those are the rules that Yahweh gave to Moses/me for husbands and wives, and for young women who are still living with their parents.
Waɗannan su ne ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Musa game da dangantakar miji da matarsa, da kuma tsakanin mahaifi da’yarsa wadda har yanzu tana a gidansa.

< Numbers 30 >