< Numbers 24 >

1 Balaam now realized that Yahweh wanted to bless the Israeli people, [not curse them]. So he did not use magic/divination [like a shaman would do] to find out what Yahweh wanted, as he often did. Instead, he turned toward the desert.
To, da Bala’am ya ga cewa Ubangiji yana jin daɗin sa wa Isra’ila albarka, bai koma wajen sihiri kamar dā ba, amma ya juya fuskarsa wajen hamada.
2 He saw the Israeli people camped there [in their tents], with each tribe gathered in its own group. Then the Spirit of God took control of him,
Da Bala’am ya duba sai ya ga Isra’ila sun yi sansani kabila, kabila, Ruhun Allah kuwa ya sauko masa,
3 and enabled him to give this prophetic message to Balak: “I, Balaam, the son of Beor, am giving this prophecy; I am speaking as a man who sees [what will happen in the future] clearly speaks.
sai ya yi annabcinsa ya ce, “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
4 I hear this message from God; I see a vision from him who is all-powerful. My eyes are open as I prostrate myself in front of him.
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, maganar wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, mutumin da ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
5 You descendants of Jacob, your tents are very beautiful; they are truly lovely!
“Ina misalin kyan tentunanka, ya Yaƙub, wuraren zamanka, ya Isra’ila!
6 Your tents are spread out [in front of me like groves of palm trees in] valleys, like gardens alongside a river. They are like strong aloe trees/plants that Yahweh has planted, like [strong] cedar trees [that grow] along the rivers.
“Kamar kwaruruka suke a shimfiɗe, kamar lambu kusa da rafi, kamar itatuwan aloyes da Ubangiji ya dasa, kamar itatuwa al’ul kusa da ruwaye.
7 Your water buckets will always be full; the seeds [that you plant] will always have plenty of water [to make them grow]. The Israelis’ king will be greater than [King] Agag; the kingdom that he rules will be honored.
Ruwa zai kwararo daga bokitinsu; irinsu za su sami ruwa a yalwace. “Sarkinsu zai fi sarkin Agag; mulkinsu zai ɗaukaka.
8 God brought the Israelis out of Egypt, [leading them along] with his great power [MTY] like a wild ox has. He devastates all the nations that oppose him; he breaks all those people’s bones into pieces, and shoots them with his arrows.
“Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfin kutunkun ɓauna. Sun cinye abokan gāban, suka kakkarya ƙasusuwansu; da kibiyoyinsu suka sossoke su.
9 The Israelis are like lions that crouch and lie down, [ready to pounce on their prey] [SIM]. They are like lionesses [that are resting, but ready to attack]; no one [RHQ] would dare to arouse them! [God] will bless everyone who blesses you Israelis, and he will curse everyone who curses you.”
Kamar zaki sun laɓe sun kwanta, kamar zakanya, wa zai yi ƙarfin hali yă tashe su? “Bari waɗanda suka albarkace ka, su sami albarka waɗanda kuma suka la’anta ka, su la’antu!”
10 Then King Balak was extremely angry with Balaam. He showed with his hands that he was very angry, and he [shouted at Balaam], “I summoned you here to curse my enemies! Instead, you have (blessed/asked God to bless) them three times!
Fushin Balak ya ƙuna a kan Bala’am. Ya tafa hannunsa, ya ce masa, “Na kira ka don ka la’anta abokan gābana, amma sai ga shi ka sa musu albarka har sau uku.
11 So now, get out of here! Go back home! I said that I would pay you a lot of money [if you cursed them], but Yahweh has prevented you from getting any pay!”
Yanzu ka bar nan ka tafi gida! Na ce zan sāka maka da lada mai kyau, amma Ubangiji ya hana ka samun ladan.”
12 Balaam said to Balak, “[Do you not remember what] [RHQ] I told the messengers that you sent to me? I said,
Bala’am ya ce wa Balak, “Ban faɗa wa’yan aikan da ka aiko wurina ba cewa,
13 ‘Even if Balak would give me a palace filled with silver and gold, I would not disobey Yahweh. I cannot do anything bad or anything that is good [that he does not approve of].’ And I told you that I could say only what Yahweh says to me.
‘Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba, kuma dole in faɗa abin da Ubangiji ya ce ne kawai’?
14 So yes, I will return to my people, but first, allow me to tell you what will happen to you Moab people in the future.”
Yanzu zan koma wajen mutanena, amma bari in gargaɗe ka game da abin da mutanen nan za su yi wa mutanenka cikin kwanaki masu zuwa.”
15 So Balaam said this [to Balak]: “I, Balaam, son of Beor, am again giving a prophecy, speaking as a man who sees [what will happen in the future] clearly speaks.
Sa’an nan ya furta saƙonsa. “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
16 I hear a message from God; I know things that God, who lives in heaven, has [revealed to me]. I see a vision from him who is all-powerful. My eyes are open as I prostrate myself in front of him.
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, wanda yake da sani daga Mafi Ɗaukaka, wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, wanda ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
17 The things that I see [in the vision] are not [going to happen] now; I see things [that God will cause to happen] in the future. A man who is [a descendant of] Jacob will appear like a star [MET]; a king who holds a scepter will be one of the Israeli people. He will crush the heads of you people of Moab; he will wipe out the descendants of Seth.
“Na gan shi, amma ba yanzu ba; na hange shi, amma ba kusa ba. Tauraro zai fito daga Yaƙub; sandan mulki zai fito daga Isra’ila. Zai ragargaje goshin Mowab, kawunan dukan’ya’yan Set.
18 The Israelis will occupy Edom, and they will conquer their enemies [who live near] Seir [Mountain]. The Israeli people will be victorious/strong.
Za a ci Edom da yaƙi; za a ci Seyir, abokiyar gābanta, amma Isra’ila zai ƙara ƙarfi.
19 A ruler who is a descendant of Jacob will come; he will get rid of the people who still live in the city [where Balaam first met Balak].”
Mai mulki zai fito daga Yaƙub yă hallaka waɗanda suka ragu a birnin.”
20 Then Balaam looked out over where the Amalek people-group [lived], and he prophesied this: “The Amalek people-group were the greatest nation, but they will be wiped out.”
Sai Bala’am ya ga Amalek, ya kuma furta maganarsa. “Amalek yana cikin al’ummai na fari, amma zai zama na ƙarshen da za a hallaka.”
21 Then he looked out over the area where the Ken people-group [lived], and he prophesied this: “You [think that] the place where you live is secure/safe like a nest that is made in the cliffs [MET],
Sai ya ga Keniyawa, ya kuma furta maganarsa. “Wurin zamanku lafiya yake, an kuma sa sheƙarku a cikin duwatsu;
22 but you will be wiped out when the army of Assyria conquers you.”
duk da haka, za a hallaka ku Keniyawa sa’ad da Asshur ya kame ku.”
23 Balaam ended his prophecies by saying, “Also, (who can (survive/escape) when God does all these things?/no one will be able to (survive/escape) when God does all these things!) [RHQ]
Sai ya furta maganarsa ya ce, “Wayyo, wa zai rayu sa’ad da Allah ya yi haka?
24 Ships will come from Cyprus [Island], and [the men in those ships] will defeat [the armies of] Assyria and Eber. But God will get rid of those men, too.”
Jiragen ruwa za su zo daga Kittim; za su murƙushe Asshur da Eber, amma su ma za a hallaka su.”
25 Then Balaam and Balak returned to their homes.
Sa’an nan Bala’am ya tashi ya koma gidan, Balak kuma ya yi tafiyarsa.

< Numbers 24 >