< Numbers 23 >

1 Balaam said to King Balak, “Build seven altars for me here. Then kill seven young bulls and seven rams [for a sacrifice].”
Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
2 So Balak did that. And then he and Balaam each burned a young bull and a ram [as a sacrifice] on each altar.
Balak ya yi yadda Bala’am ya faɗa, sai su biyu suka miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
3 Then Balaam said to Balak, “You stand here close to your burned offerings, and I will go and ask Yahweh if he has something else to tell me. Then I will tell you what he says to me.” Then Balaam went by himself to the top of a hill,
Sa’an nan Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in koma wani wurin da yake a kaɗaice. Wataƙila Ubangiji zai sadu da ni. Duk abin da ya bayyana mini, zan faɗa maka.” Sai ya haura kan wani wurin da yake a kaɗaice a tudun.
4 and God appeared to him there. Balaam said to him, “We have built seven altars, and I have killed and burned a young bull and a ram [as a sacrifice to you] on each altar.”
Allah kuwa ya sadu da Bala’am. Bala’am ya ce, “Na shirya bagadai bakwai, na kuma miƙa bijimi guda da rago guda, a kan kowane bagade.”
5 Then Yahweh gave Balaam a message to give to King Balak. Then he said, “Go back and tell him what I told you.”
Ubangiji ya ba wa Bala’am saƙo ya ce, “Ka koma wurin Balak, ka faɗa masa wannan saƙo.”
6 When Balaam returned to Balak, Balak was standing with the leaders from Moab beside the offerings he had burned [on the altar].
Saboda haka, sai Bala’am ya koma wurin Balak ya same shi tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dukan dattawan Mowab.
7 This is the message that Balaam told them: “Balak, the King of Moab, summoned me to come here from Syria; he brought me here from the hills at the eastern side of Syria. He said, ‘Come and curse the descendants of Jacob for me, saying that bad things will happen to these Israeli people!’
Sai Bala’am ya furta abin da Allah ya faɗa masa ya ce, “Balak ya kawo ni daga Aram, sarkin Mowab ya kawo ni daga gabashin duwatsu. Ya ce, ‘Zo, ka la’anta mini Yaƙub; zo, ka tsine Isra’ila.’
8 But (how can I curse people whom God has not cursed?/I certainly cannot curse people whom God has not cursed!) [RHQ] (How can I condemn people whom Yahweh has not condemned?/I cannot condemn people whom Yahweh has not condemned!) [RHQ]
Yaya zan iya la’anta waɗanda Allah bai la’anta ba? Yaya zan tsine waɗanda Ubangiji bai tsine ba?
9 I have seen them from the tops of the rocky peaks. I see that they are a group of people who live by themselves; they have separated themselves from other nations.
Daga kan duwatsu na gan su, daga bisa kan tuddai na hange su. Na ga mutane da suke zaune su kaɗai ba sa ɗauki kansu ɗaya da al’ummai ba.
10 (Who can count the descendants of Jacob; they are as numerous as particles of (dust/dirt)?/No one can count the descendants of Jacob; they are as numerous as particles of (dust/dirt)!) [RHQ] (Who can count even a quarter of the Israeli people?/No one can count even a quarter of the Israeli people!) [RHQ] I wish/hope that I will die like righteous people die; I hope that I will die [peacefully] like they will die.”
Wa zai iya ƙidaya ƙurar Yaƙub ko yă ƙidaya kashi ɗaya bisa huɗu na Isra’ila? Bari in mutu, mutuwar adali ƙarshena kuma yă zama kamar nasu!”
11 Then Balak said, “What have you done to me [RHQ]? I brought you here to curse my enemies, but instead you have (blessed them/asked Yahweh to bless them)!”
Balak ya ce wa Bala’am, “Me ke nan ka yi mini? Na kawo ka, ka la’anta abokan gābana, sai ga shi albarka kake sa musu!”
12 But Balaam replied, “I can [RHQ] say only what Yahweh tells me to say. I cannot say anything else.”
Bala’am ya ce, “Ba dole in faɗa abin da Ubangiji ya sa a bakina ba?”
13 Then King Balak told Balaam, “Come with me to another place. There you will see only part of the Israeli people, and you will be able to curse those people for me.”
Sa’an nan Balak ya ce masa, “Zo, mu tafi wani wuri inda za ka gan su; a nan kana ganin sashe ne kawai, ba dukansu ba. Daga can kuwa, ka la’anta mini su.”
14 So Balak took Balaam to a field on the top of Pisgah [Mountain]. There, again he built seven altars and offered a young bull and a ram [as a sacrifice] on each altar.
Saboda haka ya ɗauke shi zuwa filin Zofim a ƙwanƙolin Fisga, a can ya gina bagadai bakwai, ya kuma miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
15 Then Balaam said to the king, “Stand here close to your burned offerings, while I go and talk with Yahweh.”
Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in je in sadu da Ubangiji a can.”
16 So Balaam did that, and Yahweh appeared to Balaam again and gave him another message. Then he said, “Go back to Balak and tell him that message.”
Ubangiji ya sadu da Bala’am, ya kuma ba shi saƙo ya ce, “Koma wurin Balak ka ba shi wannan saƙo.”
17 So Balaam returned to where the king and the leaders from Moab were standing, next to the altar where Balak had burned the sacrifices. Balak asked him, “What did Yahweh say?”
Saboda haka ya tafi ya same Balak tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dattawan Mowab. Balak ya tambaye Bala’am ya ce, “Mene ne Ubangiji ya ce?”
18 Then Balaam told him this message: “Balak, listen carefully; hear what I have to say, you son of Zippor [DOU]!
Sai Bala’am ya furta saƙon da aka ba shi ya ce, “Tashi, Balak, ka saurara; ka kasa kunne gare ni, ɗan Ziffor.
19 God is not a human being. Humans lie, but God never lies. He never changes his mind/thoughts, as humans do. Whatever he has said that he will do, he does.
Allah ba mutum ba ne, da zai yi ƙarya, shi ba ɗan mutum ba ne, da zai canja tunaninsa. Yana maganar abin da ba zai iya aikata ba ne? Yakan kuma yi alkawarin da ba zai iya cikawa ba?
20 He commanded me [to request him] to bless [the Israelis], So he has blessed them, and I cannot change that.
Na karɓi umarni in sa albarka; na kuwa sa albarka, ba zan iya janye ta ba.
21 Yahweh their God is with/helping them; they have declared that he is their true king. So the descendants of Jacob will not be harmed; they will not have any troubles [DOU].
“Bai ga mugunta a cikin Yaƙub ba, bai kuma ga wahala a Isra’ila ba. Ubangiji Allahnsu yana tare da su; sowar Sarki yana cikinsu.
22 God brought them out of Egypt [where they were slaves]; he is as strong as a wild ox.
Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfi iri na kutunkun ɓauna.
23 When people curse [PRS] the descendants of Jacob, they will not be harmed; when people work sorcery on them, it will have no power. So now people will say about the descendants of Jacob, ‘God has done wonderful things for the Israelis!’
Ba wata maitar da za tă ci Yaƙub, ba sihiri da zai cuci Isra’ila. Yanzu za a ce game da Yaƙub da Isra’ila, ‘Duba abin da Allah ya yi!’
24 They are very strong, like lionesses that are ready to attack [other animals]; they stand firm like lions. The lions refuse to rest until they have [killed and] eaten their prey, and drunk the blood of the animals they slaughtered.”
Mutane sun tashi kamar ƙaƙƙarfar zakanya; sun tā da kansu kamar zaki wanda ba ya hutawa sai ya cinye naman abin da ya kama ya kuma sha jinin abin da ya kama.”
25 Then Balak said to Balaam, “If you will not curse them, then [I certainly] do not [want you to] bless them!”
Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Kada ka la’anta su, kada kuma ka sa musu albarka!”
26 But Balaam replied, “I told you that I must do only what Yahweh tells me to do!”
Bala’am amsa ya ce, “Ban faɗa maka zan yi kaɗai abin da Ubangiji ya ce ba?”
27 Then King Balak said to Balaam, “Come with me; I will take you to another place. Perhaps it will please God to allow you to curse them from that place.”
Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Zo in kai ka wani wuri. Wataƙila zai gamshi Allah, yă bari ka la’anta mini su daga can.”
28 So Balak took Balaam to the top of Peor [Mountain] where they could look down [and see the Israelis in] the desert.
Balak kuwa ya ɗauki Bala’am zuwa ƙwanƙolin Feyor, wanda yake fuskantar hamada.
29 Balaam again told Balak, “Build me seven altars again and kill seven young bulls and seven rams [for a sacrifice].”
Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka kuma shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
30 So Balak did what Balaam told him to do. He burned a young bull and a ram on each altar as sacrifices.
Balak ya yi yadda Bala’am ya ce, ya kuwa miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.

< Numbers 23 >