< Numbers 17 >

1 Then Yahweh said to Moses/me,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Tell the Israeli people to bring to you twelve walking sticks. They should bring one from each of the leaders of the twelve tribes. You should carve each leader’s name on his stick.
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka kuma karɓi sanduna goma sha biyu daga wurinsu, sanda guda daga kowane shugaban gidan kakanninsu. Ka rubuta sunan kowa a sandansa.
3 There must be one stick for the leader of each tribe, so you must carve Aaron’s name on the stick for the tribe of Levi.
A kan sandan Lawi kuwa ka rubuta sunan Haruna, gama dole a sami sanda ɗaya saboda shugaban gidan kakanninsu.
4 Put those sticks inside the Sacred Tent, in front of the sacred chest that has in it the tablets on which the Ten Commandments are written. That is the place where I always talk with you.
Ka ajiye su a Tentin Sujada, a gaba akwatin Alkawari, inda zan sadu da kai.
5 Buds will sprout on the stick of the man whom I have chosen [to be the priest]. [When the people see that], they will stop their constantly complaining about you [because they will realize that you are the one whom I have chosen].”
Sandan mutumin da na zaɓa zai yi toho, da haka zan raba kaina da gunagunin da Isra’ilawa suke yi.”
6 So Moses/I told the people what Yahweh had said. Then each of the twelve Israeli leaders, including Aaron, brought his walking stick to Moses/me.
Saboda haka Musa ya yi magana da Isra’ilawa, sai shugabanninsu suka ba shi sanduna goma sha biyu, sanda ɗaya don shugaba, bisa ga gidajen kakanninsu, sandan Haruna kuma yana a cikinsu.
7 Moses/I placed the sticks inside the Sacred Tent in front of the sacred chest.
Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada.
8 The following morning, when he/I went into the tent, he/I saw that Aaron’s stick, which represented the tribe of Levi, had sprouted, it had produced leaves and blossoms, and it had also produced almonds that were ripe!
Kashegari da Musa ya shiga cikin Tentin Sujada sai ga sandan Haruna na gidan Lawiyawa ya yi toho, ya yi furanni, ya kuma yi’ya’yan almon.
9 Moses/I brought all the sticks out of the Sacred Tent and showed them to the people. Each of the twelve leaders took back his own stick.
Sai Musa ya fitar wa dukan Isra’ilawa dukan sandunan da suke daga gaban Ubangiji. Suka duba, kowa kuma ya ɗauki sandansa.
10 Then Yahweh said to Moses/me, “Put Aaron’s stick in front of the sacred chest, and let it stay there permanently. That will be a warning to people who want to rebel [against me]. Then no more people will die [because of complaining against me].”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka mayar da sandan Haruna a akwatin Alkawari, don a ajiye shi alama ga masu tawaye. Wannan zai kawo ƙarshen gunaguninsu a kaina, domin kada su mutu.”
11 So Moses/I did what Yahweh had commanded.
Musa kuwa ya aikata kamar dai yadda Ubangiji ya umarce shi.
12 Then the Israeli people said to Moses/me, “We are going to die! All of us are surely going to die!
Sai Isra’ilawa suka ce wa Musa, “To, ai in haka ne, mun ƙare ke nan!
13 Everyone who comes close to Yahweh’s Sacred Tent dies. Are the rest of us going to die, also?” [RHQ]
Idan an ce duk wanda ya zo kusa da tabanakul na Ubangiji zai mutu, ai rayuwarmu kamar mun mutu ke nan.”

< Numbers 17 >