< Numbers 12 >

1 [Moses’/My older sister] Miriam and [his/my older brother] Aaron were saying this: “Is Moses the only one to whom Yahweh has spoken messages to tell to us [RHQ]? Does Yahweh not speak messages to us two also?” [They told people that] they were saying that because Moses/I had married a woman who was a descendant of the Cush people-group, [but they were really saying that because they (were jealous/did not want Moses/me to be the only leader of the Israeli people)]. But Yahweh heard what they were saying.
Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
2
Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
3 [The truth was that] Moses/I was very humble. He/I was more humble than anyone else on the earth [and Moses/I had not appointed himself/myself to be their leader].
(Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
4 So immediately Yahweh spoke to Moses/me and to Aaron and Miriam. He said, “All three of you must go and stand at the Sacred Tent.” So they/we did that.
Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
5 Then Yahweh descended to the entrance of the tent in a cloud [that resembled a huge white] pillar. He told Aaron and Miriam to step forward, so they did.
Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
6 Then he said to them, “Listen to me! When a prophet is among you, I [usually] reveal myself to him by allowing him to see visions, and I speak to him in dreams.
sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
7 But that is not the way I speak to my servant Moses. I trust that he will lead my people [well].
Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
8 So I talk to him face-to-face. I speak to him (clearly/using words that he will understand easily), not using parables. He has even seen what I look like. So you should be afraid to criticize my servant Moses!”
Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
9 Yahweh was very angry with Miriam and Aaron, and he left.
Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
10 When the cloud rose up from the Sacred Tent, Aaron looked at Miriam, and he saw that her skin was [as white] as snow, because she now had leprosy.
Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
11 Aaron said to Moses/me, “My master, please do not punish us for this sin that we have foolishly committed.
sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
12 Do not allow Miriam to be like a baby that is already dead when it is born, whose flesh is already half decayed!”
Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
13 So Moses/I cried out to Yahweh, saying, “God, I plead with you to heal her!”
Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
14 But Yahweh replied, “If her father had [rebuked her for doing something wrong by] spitting in her face, she would have been ashamed for seven days. [She should be ashamed because of what she has done]. So send her outside the camp for seven days. Then [she will not have leprosy any more, and] she may return to the camp.”
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
15 So they sent her outside the camp for seven days. (The people/We) did not move [to another location] until she returned.
Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
16 But after [she returned], they/we left Hazeroth and moved [north] in the Paran Desert and set up their/our tents there.
Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.

< Numbers 12 >