< Micah 6 >

1 Pay attention to what Yahweh says [to you Israeli people]: “Stand up [in court] and state what you are accusing [me] about. And allow the hills and mountains to hear what you will say.
Ku saurari abin da Ubangiji ya ce, “Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu; bari tuddai su ji abin da kuke so ku faɗa.
2 [But then] you mountains must [also] listen [carefully] [DOU] to what I, Yahweh, am complaining [about my people]. I have something to say about what [DOU] my Israeli people are doing that displeases me.
“Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku, ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya. Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa; yana tuhumar Isra’ila.
3 My people, what have I done to [cause trouble for] you [RHQ]? What have I done to cause you to experience difficulties? Answer me!
“Ya ku mutanena, me na yi muku? Ta yaya na nawaita muku? Ku amsa mini.
4 I [did great things for your ancestors]; I brought them out of Egypt; I rescued them from that land where they were slaves. I sent Moses to [lead] them, and [his older brother] Aaron and [his older sister] Miriam.
Na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma’yantar da ku daga ƙasar bauta. Na aika da Musa yă jagorance ku, haka ma Haruna da Miriyam.
5 My people, think about when Balak, the king of Moab, requested Beor’s son Balaam [to curse your ancestors], and think about what Balaam replied. Think about [how your ancestors crossed the Jordan River miraculously while] they were traveling from Acacia to Gilgal. [Think about those things in order] that you may know that [I], Yahweh, do what is right.”
Ya ku mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla da kuma amsar da Bala’am ɗan Beyor ya bayar. Ku tuna da tafiyarku daga Shittim zuwa Gilgal, don ku san ayyukan adalcin Ubangiji.”
6 [The Israeli people ask, ] “What shall we bring to Yahweh [who lives in] heaven when we come to him and bow down before him? Should we bring calves that are a year-old that will be offerings that will be [killed and] completely burned [on the altar]?
Da me zan zo a gaban Ubangiji in rusuna a gaban Maɗaukaki Allah? Shin, zan zo ne a gabansa da hadaya ta ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?
7 Will Yahweh be pleased [if we offer to him] 1,000 rams and 10,000 streams of [olive] oil? Should we offer our firstborn children [to be sacrifices] to pay for the sins that we have committed [DOU]?”
Ubangiji zai ji daɗin hadayar raguna dubbai da kuma rafuffukan mai dubbai goma? Zan ba da ɗan farina ne don laifina, ko’ya’yan jikina domin zunubin raina?
8 [No, because] he has shown each of us what is good [to do]; he has shown [RHQ] us what he requires each of us [to do]: He wants us to do what is just/fair and to love and to be merciful [to others], and [he wants us] to live humbly [while we fellowship] with him, our God.
Ya nuna maka, ya mutum, abin da yake mai kyau. Me Ubangiji yake bukata daga gare ka kuwa shi ne ka yi gaskiya ka so aikata jinƙai ka kuma yi tafiya da tawali’u a gaban Allah.
9 “I am Yahweh, so if you are wise, you should revere me. I am calling out to [you people of] Jerusalem, ‘The armies [MET] that will destroy your city are coming, so pay careful attention to me, the one who is causing them to punish you with my rod.
Ku saurara! Ubangiji yana kira ga birni, a ji tsoron sunana kuwa hikima ce, “Ku kasa kunne ga sandan nan da kuma wannan wanda ya naɗa.
10 Do you think that [RHQ] I should forget that you wicked people filled your homes with valuable things that you acquired by cheating [others]? Do you think that [RHQ] I should forget that you used false measures [when you bought and sold things]? Those are things that I hate.
Har yanzu zan manta, ya muguwar gida da dukiyarki da kika samu a muguwar hanya zan kuma manta da bugaggen mudun awo wanda ake zargi?
11 [Do you think] that [RHQ] I should say nothing about people who use scales that do not weigh correctly, and who use weights that are not accurate?
Zan kuɓutar da mutumin da yake da ma’auni na rashin gaskiya, da kuma buhun ma’aunan ƙarya?
12 The rich people among you always act violently [to get money from poor people]. All of the people [in Jerusalem] are liars, and they [SYN] always deceive people.
Attajiranta masu fitina ne; mutanenta kuma maƙaryata ne harsunansu kuwa suna yaudara.
13 Therefore, I have [already] begun to get rid of you, to ruin you because of the sins that you have committed.
Saboda haka, zan hallaka ku in lalace ku saboda zunubanku.
14 [Soon] you will eat food, but you will not have enough to satisfy you; your stomachs will [still feel as though they are] empty. You will try to save up [money], but you will not be able to save anything, because I will send your enemies to take it from you in wars [MTY].
Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba, cikinku zai zama babu kome Za ku tattara amma ba za ku yi ajiyar kome ba, gama abin da kuka yi ajiya zan ba wa takobi.
15 You will plant [seeds], but you will not harvest [anything]. You will press olives, but [others], not you, will use the [olive] oil. You will trample on grapes [and make wine from the juice], but [others], not you, will drink the wine.
Za ku yi shuki amma ba za ku girba ba; za ku matse zaitun amma ba za ku yi amfani da mai wa kanku ba, za ku tattaka’ya’yan inabi amma ba za ku sha ruwan inabin ba.
16 [Those things will happen to you because] you obey [only] the wicked laws of [King] Omri, and [you do the terrible things that wicked King] Ahab and his descendants commanded. So, I will destroy your [country], and I will cause your people to be despised; people [of other nations] will insult you.’”
Kuna kiyaye ƙa’idodin Omri da dukan ayyukan gidan Ahab kun kuma bi al’adunsu. Saboda haka, zan maishe ku kufai in mai da ku abin dariya a cikin mutane, za ku sha reni a wurin al’ummai.”

< Micah 6 >