< Malachi 1 >

1 [This is] the message that Yahweh gave to [the prophet] Malachi to [give to the people of] Israel.
Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
2 Yahweh says, “I have [always] loved you [Israeli people].”
“Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
3 But you reply, “In what way have you loved us?” Yahweh replies, “[This is how I loved you]: [It is true that your ancestor] Jacob was [RHQ] Esau’s [younger] brother, and I loved Jacob, but I rejected Esau. I caused his hilly region to become (desolate/a place where crops did not grow). I caused the land which he possessed to become a desert where jackals/wolves live.”
amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
4 [The descendants of Esau who live in] Edom may say, “[Yes, ] we have been crushed/ruined, but we will rebuild [houses] in the ruins.” But the Commander of the armies of angels replies, “They may build [houses again], but I will demolish [them again]. Their [country] will be called ‘The land where wicked people [live]’ and [their people will be called] ‘The people with whom Yahweh is angry forever’.”
Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
5 When you [Israeli] people yourselves see [what I will do to them], you will say, “[It is evident far] beyond the borders of Israel that Yahweh is [very] great!”
Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
6 But the Commander of the armies of angels says to the priests, “Boys honor their fathers, and servants [respect] their masters. So, if I am [like your] father and your master, why [RHQ] do you not honor and respect me? You have despised me [MTY]!” But you ask, “(How/In what way) have we despised you?”
“Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
7 [Yahweh replies, ] “[Instead of honoring me, you have despised me] by offering sacrifices on my altar that are unacceptable to me.” Then you ask, “What sacrifices have we given that have been unacceptable to you?” [Yahweh replies, ] “You think that (it does not matter/it is okay) if you do not respect my altar.
“Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
8 You offer for sacrifices animals that are blind. (Is that not wrong?/That is disgusting!) [RHQ] And you offer for sacrifices animals that are crippled or that have diseases. (Is that also not wrong?/That [also] is disgusting!) [RHQ] If you tried to give presents like that to your governor, (do you think [RHQ] that he would be pleased?/he would certainly not be pleased!) (Would he [RHQ] accept such gifts? He would certainly not accept such gifts!) [That is what] the Commander of the armies of angels says!”
Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 [And he also says, ] “You plead with me to be merciful to you. But you bring to me sacrifices that are not acceptable to me, so why should I be kind to you [RHQ]?”
“To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
10 The Commander of the armies of angels [also] says, “I wish/desire that one of you would shut the gates [of the temple courtyard], in order that no one could offer those worthless sacrifices. I am not pleased with you, and I will not accept the offerings that you bring to me.
“Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 [People of other] nations honor me [MTY] [every day], from sunrise/morning until sunset/evening. All over the world people offer incense and [other] pure/acceptable offerings to me [MTY]. [They do that] because [people among all] the nations know that I [MTY] am [very] great.
Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 But you [priests show that you] despise me [by what you do]. You say, ‘[It is all right if] people pollute the altar by bringing sacrifices that are unacceptable.’
“Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
13 You say ‘We are tired of [burning all these sacrifices on the altar].’ You (turn up your noses at/act very disrespectfully toward) [me]. When you bring [to me] animals that have been stolen or ones that are crippled or that have diseases, to offer them for sacrifices, [do you think that] [RHQ] I should accept them?
Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
14 [I will] curse anyone who [tries to] cheat [me] by solemnly promising [to bring to me a perfect] ram from his flock [of sheep] and then brings to me one that has defects. [If anyone does that, I will punish him], because I am a great king; [I am] the Commander of the armies of angels and [people of the other] nations revere me [MTY], [but you do not]!”
“La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.

< Malachi 1 >