< Luke 4 >

1 As Jesus left the Jordan [River valley], the Holy Spirit was completely controlling him.
Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji
2 For 40 days the Spirit led him around in the desolate area. During that time Jesus was being tempted by the devil {the devil was tempting him}, and Jesus did not eat anything. When that time ended, he was [very] hungry.
kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.
3 Then the devil said to Jesus, “Because you [claim that you] ([have a relationship with] God as a son [has with his father] [MET]/are the man who is both God and man), [prove it by] telling these stones to become bread [so that you can eat them]!”
Shaidan ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa.”
4 Jesus replied, “[No, I will not change stones into bread, because it is written] {[Moses] wrote} [in the Scriptures] that [eating] food sustains people physically, but it does not [sustain them spiritually. They also need food for their spirits].”
Yesu ya amsa masa, “A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'”
5 Then the devil took him on top of [a high mountain] and showed him in an instant all the nations in the world.
Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci.
6 Then he said to [Jesus], “I will give you the authority [to rule] all these areas and will make you famous. [I can do this] because [God] has permitted me [to control these areas], and I can allow anyone I desire to rule them!
Shaidan ya ce masa, “Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama.
7 So if you worship me, I will [let] you [rule] them all!”
Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka.”
8 But Jesus replied, “[No, I] will not [worship you, because] it is written {[the Psalmist] wrote} [in the Scriptures], ‘It is the Lord, your God, whom you must worship, and you must serve only him!’”
Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa.”
9 Then the devil took [Jesus] to Jerusalem. He set him on the highest part of the Temple and said to him, “Because you [claim that you] ([have a relationship with God as a son has with his father] [MET]/are the man who is both God and man), [prove it by] jumping down from here.
Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan.
10 [You will not be hurt], because it is written {the [Psalmist] wrote} [in the Scriptures], ‘God will command his angels to protect you [(sg)].
Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,'
11 They will lift you up with their hands [when you are falling], so that [you will not get hurt]. You will not [even] strike your foot on a stone.’”
kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse.”
12 But Jesus replied, “[No, I] will not [do that, because] it is written {[Moses] wrote} [in the Scriptures]: ‘Do not try to test the Lord your God [to see if he will prevent something bad from happening to you when you do something foolish]’.”
Yesu ya amsa masa cewa, “An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'”
13 Then, after the devil had finished trying to tempt [Jesus] in many ways, he left him. He wanted to try to tempt him later at an appropriate time.
Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.
14 As the Spirit empowered him, Jesus returned to Galilee [district. People] throughout all that region heard about what he [was doing].
Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin.
15 He taught [people] in their (synagogues/meeting places). [As a result], he was praised by everyone {everyone praised him}.
Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.
16 Then [Jesus] went to Nazareth, [the town] where he grew up. (On the Sabbath/On the Jewish rest day) he went (to the synagogue/to the Jewish meeting place), as he usually did. He stood up [to indicate that he wanted] to read [Scriptures] to them.
Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi.
17 A scroll containing [the words] that the prophet Isaiah [had written] was given to him {[Someone] gave to him a scroll containing [the words] that the prophet Isaiah [had written]}. He opened the scroll and found the place from which he [wanted to] read. [He read these words]:
An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,
18 The Spirit (of the Lord/of God) is upon me. He has appointed [MTY] me to declare God’s good news to the poor. He has sent me [here] to proclaim that God will deliver those whom [Satan] has captured, and he will [enable me to] enable those who are blind to see. He will enable me to free people who have been oppressed {whom [others] have oppressed}.
“Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci,
19 And he sent me to declare that now is the time when (the Lord/God) will [act] favorably [toward people].
in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji.”
20 Then he rolled up the scroll and gave it back to the attendant, and sat down [to teach the people]. Everyone in the synagogue was looking intently [MTY] at him.
Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa.
21 He said to them, “Today as you have been hearing [MTY] [me speak], [I am beginning] to fulfill this Scripture passage.”
Sai ya fara masu magana, “Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku.”
22 [At first] everyone there spoke well about him, and they were amazed at the charming words that he spoke. [But then some of] them said, “(He is [only] Joseph’s son!/Isn’t he [only] Joseph’s son?) [RHQ] [So] ([it is useless for us(exc) to listen to what he says!/why should we(exc) listen to what he says]?) [RHQ]”
Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, “Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?”
23 He said to them, “Surely [some of] you will quote to me the proverb that says, ‘Doctor, heal yourself!’ [What you will mean is], ‘People told us that you did miracles in Capernaum [town, but we(exc) do not know if those reports are true. So] do miracles here in your own hometown, too!’”
Yesu ya ce masu, “Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'”
24 Then he said, “It is certainly true that [people] do not accept [the message of] a prophet when he speaks in his hometown, [just like you(pl) are not accepting my message now].
Ya sake cewa, “Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.
25 But think about this: There were many widows in Israel during the time when [the prophet] Elijah [lived. During that time], because of there being no rain [MTY] for three years and six months, there was a great famine throughout the country.
Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar.
26 But [God] did not send Elijah to [help] any of those [Jewish] widows. [God sent him] to Zarepath [town] near Sidon [city], to [help] a [non-Jewish] widow.
Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon.
27 There were also many [Jewish] lepers in Israel during the time when the prophet Elisha [lived]. But [Elisha] did not heal any of them. He healed only Naaman, a [non-Jewish] man from Syria.”
Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.
28 When all the people in the synagogue heard him say that, they were very angry, [because they realized that he was inferring that he similarly would help non-Jewish people instead of helping Jews] (OR, [that they also were not worthy of receiving God’s help]).
Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka.
29 So they all got up and shoved him out of the town. They took him to the top of the hill outside their town in order to throw him off the cliff [and kill him].
Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa.
30 But he [simply] walked through their midst and went away.
Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
31 [One day] Jesus went [with his disciples] down to Capernaum, a town in Galilee [district]. On the next (Sabbath/Jewish day of rest) (OR, Each (Sabbath/Jewish day of rest)), he taught the people ([in the synagogue/in the Jewish meeting place]).
Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a.
32 They were continually amazed at what he was teaching, because [he spoke] ([with authority/as people speak who have] the right to command others what to do).
Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
33 [That day], (OR, On one of those Jewish days of rest, ) there was a man in the synagogue who was controlled by an evil spirit. That man shouted very loudly,
A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya,
34 “Hey! Jesus, from Nazareth! [We(exc) evil spirits] have nothing in common with you, so ([do not interfere with us now!/why should you interfere with us now]?) [RHQ] (Do not destroy us [now!]/Have you come to destroy us [now]?) [RHQ] I know who you are. You are the Holy One [who has come] from God!”
“Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!”
35 Jesus rebuked [the evil spirit], saying, “Be quiet! And come out [of the man]!” The demon threw the man down on the ground in the midst of the people. But without harming the man, the demon left him.
Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, “Yi shiru ka fita daga cikinsa!” Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba.
36 The people were all amazed. They said to each other, “(What he says to the demons [has great power!/] [kind of] teaching is this?) [RHQ] He speaks to them like he knows that they must obey him, and as a result they leave people!”
Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, “Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita.”
37 The people were telling everyone in [every village] in the surrounding region what Jesus [had done].
Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.
38 Jesus [and his disciples] left (the synagogue/the Jewish meeting place) and entered Simon’s house. Simon’s mother-in-law was sick and had a high fever. So [others in Simon’s family] (OR, [the disciples]) asked Jesus to [heal] her.
Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta.
39 So he bent over her and commanded the fever to leave her. At once she became well! She got up and served them [some food].
Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.
40 When the sun was setting [that day, and the restriction about not traveling] (on [the Sabbath/on the Jewish rest day]) [was ended], many people [HYP] whose [friends or relatives] were sick or who had various diseases brought them to Jesus. He put his hands on them and healed [all of] them.
Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su.
41 He also was [expelling demons] from many people. As the demons left those people, they shouted to Jesus, “You are (the Son of God/the one who is God and man)!” But he rebuked those demons and would not allow them to tell [people about him], because they knew that he was the Messiah, and [for various reasons he did not want everyone to know that yet].
Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, “Kai ne Dan Allah!” Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.
42 [Early] the next morning [Jesus] left that house and went to an uninhabited place [to pray]. Many people searched for him, and when they found him they kept urging him not to leave them.
Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su.
43 But he said to them, “I must tell [people] in other towns also the good message about how God wants to rule [MET] their lives, because that is what I was sent {[God] sent me} to do.”
Amma ya ce masu, “Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan.”
44 So he kept preaching in (the synagogues/Jewish worship places) [in various towns] in Judea [province].
Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.

< Luke 4 >