< Lamentations 3 >

1 I [, the one who am writing this, ] am a man who has been afflicted/punished [MTY] by Yahweh because he was angry.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 [It was as though] he caused me to walk in a very dark place without any light [at all].
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 He has punished [IDM] me many times, all day, [every] day.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 He has caused my skin and my flesh to become old. He has broken my bones.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 He has surrounded me [DOU] with bitterness and suffering.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 [It is as though] he has buried me in a dark place like [SIM] [the graves of] those who have been dead for a long time.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 [It is as though] [MET] he has built a wall around me, and fastened/tied me with heavy chains, and I cannot escape.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Although I call out and cry out for him to help me, he does not pay attention to my prayers.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 [It is as though] he has blocked my path with a [high] stone [wall] and has caused my path to become crooked.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 He has waited to attack me like [SIM] a bear or a lion hides and waits [to attack other animals].
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 [It is as though] he has dragged me off the path and (mauled me/torn me into pieces), and left me without help.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 [It is as though] [MET] he bent his bow and caused me to become the target [at which he shot] his arrows.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 [It is as though] he shot his arrows deep into my body.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 All my relatives laugh at me; all day, [every] day they sing songs that make fun of me.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 He has filled me with (bitterness/great suffering), [like] [MET] someone who drinks a very bitter liquid suffers.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 [It is as though] he has caused me to chew gravel that broke my teeth, and he has trampled me in the dirt.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 Things no longer go well for me; I no longer remember being prosperous.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 I [continued to] say [to myself], “I no longer expect to live much longer; I no longer confidently expect [to receive good things] from Yahweh!”
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 When I think about my suffering and my wandering [away from home], [it is like drinking] a very bitter [DOU] liquid.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 I will never forget this time when I feel very depressed/discouraged [IDM].
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 However, I confidently expect [Yahweh to do good things for me again] when I think about this:
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Yahweh never stops faithfully loving [us], and he never stops being kind to us.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 [He is the one whom we can] always trust/lean on. Every morning he is merciful [to us again].
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 [So] I say to myself, “Yahweh is all that I need; so I will confidently wait for him [to do good things for me].”
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Yahweh is good to [all] those who depend on him, to those who seek his [help].
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 [So] it is good for us to wait quietly for Yahweh to save/rescue [us].
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 And it is good for us to [patiently] endure [suffering] while we are young.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Those [who seek his help] should sit by themselves, silently, [knowing that] it is Yahweh who has allowed/caused them to suffer.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 They should lie in the dirt, with their faces on the ground, [because] they can still hope [that Yahweh will help them].
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 If someone strikes us on one cheek, we should turn the other cheek toward that person [in order that he may strike it, too], and accept/endure it when we are insulted.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Yahweh does not abandon [us his people] forever.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Sometimes he causes us to suffer, but sometimes he is kind [to us] because he continually and faithfully loves [us].
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 And he is not happy about causing human beings to suffer or to be sad.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 If people (mistreat all the prisoners/crush all the prisoners under their feet)
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 or if they rebel against God by refusing to give to people the things that it is right for them [to receive],
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 or if they cause judges to decide matters unjustly, (does Yahweh not see all those things?/Yahweh certainly sees all those things!) [RHQ]
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 No one can [RHQ] command something to happen [and then cause it to happen] if Yahweh has not already decided that it should happen.
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 God in heaven [MTY] is [RHQ] the one who causes disasters to happen, and he [also] causes good things to happen.
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 [So] it is certainly not [RHQ] right for us, who are only humans, to complain when he punishes us for the sins that we have committed.
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Instead, we should (examine/think carefully about) our behavior; we should turn back to Yahweh.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 We should pray [IDM] sincerely and lift up our arms toward God in heaven, [and say, ]
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 “We have sinned and rebelled [against you], and you have not forgiven [us].
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 You have surrounded us with your anger and pursued us; you have slaughtered [us] without pitying us.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 You have hidden yourself in a cloud, with the result that you do not hear [us] when we pray.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 You have caused [the people of other] nations to consider us to be only garbage [DOU].
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 All our enemies have insulted us.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 We are constantly afraid [DOU], [because] we have experienced disasters and ruin [DOU].”
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 I cry a lot because my people have been destroyed.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 My tears continually flow; they will not stop
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 until Yahweh looks down from heaven and sees [us].
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 I am very grieved because of [what has happened to] the women of my city.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Those who are my enemies hunted for me like [SIM] [people hunt for] a bird [to kill it] [even though] there was no reason [for them to do that].
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 They threw me into a pit to kill me, and they threw stones on top of me.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 The water [in the pit] rose above my head, and I said [to myself], “I am about to die/drown!”
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 But from the bottom of the pit I cried out to you [MTY], “Yahweh, [help me]!”
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 I pleaded with you, “Do not refuse to heed [MTY] me while I cry out to you!”
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Then you answered me and said, “Do not be afraid!”
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Yahweh, you defended me; you did not allow me to die.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 [Now], Yahweh, you have seen the evil things that my enemies have done to me, [so] decide my case [and show that I am right]!
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 You know the evil things that they have planned to do to me.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Yahweh, you have heard them insult [me] and what they have planned to do to me.
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 Every day they whisper and mutter things about me, all day long.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Look at them! Whether they are standing or sitting they make fun of me with the songs that they sing.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Yahweh, cause them to suffer in return for their causing [me] to suffer!
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Curse them [IDM] [for] their being very stubborn [IDM].
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Because you are angry with them, pursue them and get rid of them, [until none of them remain] on the earth.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Lamentations 3 >