< Judges 2 >

1 Yahweh [appeared in the form of] an angel [and] went up from Gilgal to [a place that was later called] Bokim. He said [to the Israeli people], “I brought your [ancestors] up here from Egypt. I led them into this land that I solemnly promised to give to your ancestors. I said to them, ‘The agreement that I made with you, as for me, I will never (break it/say that it is ended).
Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
2 But as for you, you must never make a peace agreement with the people who live in this land. You must tear down the altars [where they make sacrifices to idols].’ But you have not obeyed me.
ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
3 So now, I am telling you that I will not expel [your enemies] as you advance. They will be like thorns in your sides. And [they] will try to trap you [by making you worship] their idols.”
Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
4 After he told that to all the Israelis, the people cried loudly.
Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
5 They called that place Bokim, [which means ‘weeping’]. There they offered sacrifices to Yahweh.
sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
6 After Joshua sent the Israeli people away, each group went to possess the land that had been allotted to them.
Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
7 They served Yahweh as long as Joshua was alive, and as long as the elders, those who had seen all the great things that Yahweh had done for Israel, were alive.
Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
8 Then Yahweh’s servant Joshua died. He was 110 years old when he died.
Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
9 They buried his body in the area he had received [from Moses], at Timnath-Serah, in the area where the descendants of Ephraim lived, north of Gaash Mountain.
Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
10 After all the people died who lived at the same time as Joshua [EUP], a group of people grew up who did not know Yahweh, and did not know what great things he had done for the Israeli people.
Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
11 They did things that Yahweh said were very evil. They worshiped [idols that represented the god] Baal and the goddess Astarte. They worshiped [DOU] the various gods that the people-groups around them worshiped. They stopped worshiping Yahweh, the God their ancestors worshiped, the one who had brought their ancestors out of Egypt. That caused Yahweh to be very angry.
Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
14 So he allowed people from other groups to raid them and steal their crops and animals. They were no longer able to resist their enemies, and Yahweh allowed all their enemies around them to defeat them.
Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
15 Whenever the Israelis went to fight [their enemies], Yahweh [MTY] was opposing them, and allowed their enemies to defeat them, just as he had promised he would do. So the Israelis were greatly distressed.
Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
16 Then Yahweh gave leaders to them. These leaders rescued the Israelis from the people who were raiding them.
Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
17 But the Israelis still would not pay attention to their leaders. Instead, they went to the idols, [acting like] prostitutes [who gave themselves to men who were not their husbands] [MET], and they worshiped those idols. They were not like their ancestors. Their ancestors obeyed what Yahweh commanded, but their descendants quickly stopped behaving as their ancestors had behaved.
Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
18 Whenever Yahweh gave a leader to them, he helped that leader and enabled him to rescue the people from their enemies. He helped them like that as long as that leader was alive. Yahweh pitied them as they groaned because they were being oppressed and caused to suffer.
Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
19 But after that leader died, the people went back to behaving in ways even more evil than their ancestors had behaved. They worshiped other gods and bowed down to them and did all [LIT] the things that they thought those gods wanted them to do.
Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
20 So Yahweh was very angry with the Israeli people. He said, “These people have disobeyed the agreement I made with their ancestors. They have not done what I told them to do.
Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
21 So I will no longer expel the people-groups that Joshua left in this land when he died.
ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
22 I will use them to test the Israeli people to see whether they will do what I want them to do, as their ancestors did.”
Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
23 Yahweh had allowed those people-groups to stay in that land. He did not expel them by allowing Joshua [and his men] to defeat them.
Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.

< Judges 2 >