< Judges 15 >

1 During the time that they harvested wheat, Samson took a young goat to Timnah as a present for his wife. He planned to sleep with [EUP] his wife, but her father would not let him go into [her room].
Daga baya, a lokacin girbin alkama, Samson ya ɗauki ɗan akuya ya tafi yă ziyarci matarsa. Sai ya ce, “Zan in shiga ɗakin matata.” Amma mahaifinta ya hana shi shiga.
2 He said to Samson, “I really thought that you hated her. So I gave her to the man who had been your best man at the wedding, and she married him. But look, her younger sister is [RHQ] more beautiful than she is. You can marry her!”
Ya ce wa, “Na tabbata ba ka sonta sam-sam, don haka na ba da ita ga abokinka. Ba ƙanuwarta ta fi kyau ba? Ka ɗauke ta a maimako.”
3 Samson replied, “No! And this time I have a right to get revenge on you Philistines!”
Samson kuwa ya ce musu, “A wannan lokaci ina da iko in rama a kan Filistiyawa; tabbatacce zan ji musu.”
4 Then he went out [into the fields] and caught 300 foxes. He tied their tails together, two-by-two. He fastened torches to each pair of tails.
Saboda haka ya tafi ya kama yanyawa ɗari uku ya ɗaura wutsiyoyinsu wutsiya da wutsiya. Sa’an nan ya daure acibalbal a tsakanin ko waɗanne wutsiya biyu,
5 Then he lit the torches and let the foxes run through the fields of the Philistines. The fire [from the torches] burned all the grain to the ground, including the grain that had been cut and piled in bundles. The fire also burned down their grapevines and their olive trees.
sai ya sa wa acibalbal wuta, ya saki yanyawan suka shiga gonakin Filistiyawa. Suka ƙone dammunan hatsi da hatsin da yake tsaye, tare da gonakin inabi da na zaitun.
6 The Philistines asked, “Who did this?” Someone told them, “Samson did it. He married a woman from Timnah, but then his father-in-law gave her to the man who was Samson’s best man at the wedding, and she married him.” So the Philistines went [to Timnah] and got the woman and her father, and burned them to death.
Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Wane ne ya yi wannan abu?” Sai aka ce musu, “Ai, Samson ne surukin mutumin Timna, domin an ba wa abokinsa matarsa.” Saboda haka Filistiyawa suka haura suka je suka ƙone ta da mahaifinta ƙurmus da wuta.
7 Samson [found out about that, and he] said to them, “Because you have done this, I will not stop until I get revenge on you!”
Samson ya ce musu, “Tun da kun aikata wannan, ba zan bari ba har sai na ɗau fansa a kanku.”
8 So he attacked the Philistines furiously, and killed many of them. Then he went [to hide] in a cave in the large rock at a place called Etam.
Ya kuwa fāɗa musu ya kuma karkashe su da yawa. Sa’an nan ya gangara ya zauna a kogo a dutsen Etam.
9 The Philistines [did not know where he was, so they] went up to where the descendants of Judah lived, set up their tents near Lehi [town and then raided the town].
Filistiyawa suka haura suka yi sansani a Yahuda, suka bazu kusa da Lehi.
10 The men there asked the Philistines, “Why have you attacked us?” The Philistines replied, “We have come to capture Samson. We have come to get revenge on him for what he did to us.”
Mutanen Yahuda suka ce, “Me ya sa kuka zo mana da yaƙi?” Sai suka ce, “Mun zo ne mu kama Samson, a matsayin fursunan yaƙi, mu yi masa kamar yadda ya yi mana.”
11 [Someone there knew where Samson was hiding]. So 3,000 men from Judah went down to get Samson at the cave in the rock where he was hiding. They said to Samson, “Do you not realize that the people of Philistia are ruling over us? Do you not realize what they will do to us?” Samson replied, “The only thing I did was that I got revenge on them for what they did to me.”
Sa’an nan mutane dubu uku daga Yahuda suka gangara wajen Samson a kogo a dutsen Etam. Suka ce masa, “Ba ka san cewa Filistiyawa ne suke mulkinmu ba? Me ke nan ka yi mana?” Ya ce musu, “Na ɗan yi musu abin da suka yi mini ne.”
12 But the men from Judah said to him, “We have come to tie you up and put you in the hands of the Philistines.” Samson said, “All right, but promise me that you yourselves will not kill me!”
Suka ce masa, “To, mun zo ne mu daure ka mu kai wa Filistiyawa.” Samson ya ce, “Ku rantse mini ba za ku kashe ni da kanku ba.”
13 They replied, “We will just tie you up and take you to the Philistines. We will not kill you.” So they tied him with two new ropes, and led him away from the cave.
Suka ce, “Mun yarda, za mu dai daure ka mu ba da kai gare su. Ba za mu kashe ka ba.” Saboda haka suka daure shi da sababbin igiyoyi biyu, suka saukar da shi daga dutsen.
14 When they arrived at Lehi, the Philistines came toward him, shouting [triumphantly]. But Yahweh’s Spirit came upon Samson powerfully. He snapped the ropes on his arms as easily as if they were stalks of burned flax, and the ropes fell off his wrists.
Yayinda ya zo gab da Lehi, sai Filistiyawa suka sheƙo a guje da ihu suka nufo shi. Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko da iko a kansa. Igiyoyin da suke daure a hannuwansa kuwa suka zama kamar abin da wuta ta babbaka, suka tsintsinke suka zuba daga hannuwansa.
15 Then he saw a donkey’s jawbone lying on the ground. It was fresh, [so it was hard]. He picked it up and killed about 1,000 Philistine men with it.
Da ya samo muƙamuƙin jaki, ya ɗauka, sai ya karkashe mutane dubu ɗaya.
16 Then Samson wrote this poem: “With the jawbone of a donkey I have made them like a heap of [dead] donkeys. With the jawbone of a donkey I killed 1,000 men.”
Sa’an nan Samson ya ce, “Da muƙamuƙin jaki na mai da su jakuna. Da muƙamuƙin jaki na kashe mutum dubu.”
17 When he finished killing those men, he threw the jawbone away, and later that place was called Jawbone Hill.
Da ya gama magana, sai ya jefar da muƙamuƙin; aka ba wa wannan wuri suna Ramat Lehi.
18 Then Samson was very thirsty, so he called out to Yahweh, “You have given me strength to win a great victory. So now must I die because of being thirsty, with the result that those heathen Philistines will take away my body [and mutilate it]?”
Saboda ƙishirwa ta kama shi ƙwarai, sai ya ce wa Ubangiji, “Ka ba bawanka wannan babbar nasara. To, sai in mutu da ƙishirwa, har in shiga a hannun marasa kaciyan nan su kashe ni?”
19 So God caused water to gush out of a depression in the ground at Lehi. Samson drank from it and soon felt strong again. He named that place ‘The spring of the one who called out’. That spring is still there at Lehi.
Sa’an nan Allah ya buɗe wani rami a Lehi, ruwa kuwa ya fito daga ciki. Da Samson ya sha, sai ƙarfinsa ya dawo, ya kuma wartsake. Aka sa wa wannan maɓulɓula suna En Hakkore, yana nan a Lehi har wa yau.
20 Samson was the leader of the Israeli people for 20 years, but during that time the Philistines [were the ones who really ruled over the land].
Samson kuwa ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin a zamanin Filistiyawa.

< Judges 15 >