< Joshua 7 >

1 Yahweh had commanded that all the things [that they had captured in Jericho] should be [destroyed to show that they belong] to him. But there was a man from the tribe of Judah named Achan. He was the son of Carmi and grandson of Zabdi and great-grandson of Zerah. He disobeyed [what] Yahweh [had commanded] and took for himself some of those things. So Yahweh was very angry with the Israelis.
Amma Isra’ilawa ba su yi aminci game da kayan da aka hallaka ba; Akan ɗan Karmi, ɗan Zabdi, ɗan Zera, na kabilan Yahuda ya kwashi waɗansu abubuwa, saboda haka fushin Ubangiji ya sauka a kan Isra’ilawa.
2 Joshua told some of his men to go from Jericho to Ai [town], which was east of Bethel [city] and near Beth-Aven [town]. He said to them, “Go to Ai and (spy out the area/see what the area is like).” So the men went.
Sai Yoshuwa ya aika mutane daga Yeriko zuwa Ai kusa da Bet-Awen gabas da Betel, ya ce musu, “Ku je ku leƙo ku ga yadda yankin yake.” Sai mutanen suka je suka leƙo asirin ƙasar Ai.
3 When they returned to Joshua they said, “There are only a few people in Ai. So we do not need to send all of our soldiers to defeat them. Send 2.000 or 3,000 men to attack them. That will be enough.”
Da suka dawo wurin Yoshuwa suka ce, “Ba lalle dukan jama’a su je yaƙi da Ai ba, ka aika mutum dubu biyu ko dubu uku su je su ciwo ƙasar da yaƙi, ba sai ka dami mutane duka ba, gama mutanen wurin kaɗan ne.”
4 So about 3,000 Israeli men went [to attack Ai]. But the men of Ai defeated them badly.
Saboda haka sai kimanin mutum duba uku suka haura; amma mutanen Ai suka fatattake su,
5 They killed about 36 Israelis and chased the rest of Israeli men from the city gate to the bottom of the hill. When the other Israelis saw that this had happened, they became very discouraged.
suka kashe Isra’ilawa wajen mutum talatin da shida, suka fafari Isra’ilawa tun daga bakin ƙofar birnin har zuwa wurin da ake fasa duwatsu. Suka karkashe su a gangare. Wannan ya sa zuciyar Isra’ilawa ta narke suka zama kamar ruwa.
6 Joshua and the other Israeli leaders tore their clothes [because they were very sad about being defeated]. They prostrated themselves on the ground in front of [the Sacred Tent in which was] the sacred chest. They stayed there until that evening. They also threw dirt on their heads [to show that they were very sad about what had happened].
Sai Yoshuwa ya yaga tufafinsa ya fāɗi rubda ciki a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, yana can har yamma. Dattawan Isra’ila ma suka yi haka, suka zuba toka a kawunansu.
7 Then Joshua prayed and said, “Lord God, you brought us Israelis [safely] across the Jordan River. So why are you now allowing the Amor people-group to defeat us [RHQ]? [This would not have happened] if we had stayed on the other side of the Jordan River!
Yoshuwa kuma ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, me ya sa ka sa mutanen nan suka ƙetare Urdun don ka bari mu shiga hannun Amoriyawa su hallaka mu? Kila da mun haƙura mun zauna a ɗaya gefen Urdun da ya fi mana!
8 Lord, we Israelis have been defeated by our enemies, so I do not know what to say now [RHQ].
Ya Ubangiji me zan ce, yanzu da abokan gāban Isra’ilawa suka ci ƙarfinsu?
9 The Canaan people-group and all the other people who are living in this land will hear about this. Then they will surround us and kill all of us! Then what will you do (to defend your reputation [MTY]/to show that you are a powerful God)?”
Yanzu Kan’aniyawa da sauran jama’a za su ji, za su zo su kewaye mu su share sunanmu daga duniya. To, yanzu me za ka yi don girman sunanka?”
10 But Yahweh said to Joshua, “Stand up! Stop lying there with your face on the ground [RHQ]!
Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka tashi! Me kake yi kwance rubda ciki?
11 You Israelis have sinned! You have disobeyed the commands that I told you to obey. [One of] your men has taken some of the things that I told you to destroy. He has stolen them and taken them for himself and lied [about it].
Isra’ilawa sun yi zunubi, sun karya sharaɗin da na yi musu. Sun ɗauki waɗansu abubuwan da aka keɓe; sun yi sata, sun yi ƙarya, sun ɓoye su cikin kayansu.
12 That is why you Israelis have been unable to be strong when you went to attack your enemies. That is why you have run away from them. And now you yourselves may be destroyed. If you do not do as I commanded you and destroy everything [that you captured in Jericho] I will not help you any more!”
Shi ne ya sa Isra’ilawa suka kāsa yin tsayayya da abokan gābansu; suka juya suka gudu domin za a hallaka su. Ba zan sāke kasancewa tare da ku ba sai in kun hallaka duk abin da aka keɓe don hallaka.
13 “Now go and tell this to the people: ‘Tomorrow you must [perform the rituals that will] cause yourselves to become acceptable to Yahweh again. Yahweh, the God whom we Israelis [worship], says that one of you has kept things that he told you to destroy. You will never defeat your enemies until you get rid of those things.
“Tashi, ka je ka tsarkake mutane. Ka ce musu su tsarkake kansu, su yi shiri domin gobe; gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, a cikinku akwai abubuwan da aka keɓe, ya Isra’ilawa. Ba za ku iya yin tsayayya da abokan gābanku ba sai in kun rabu da abubuwan nan da aka haramta.
14 ‘Tomorrow morning you must present yourselves before Yahweh, tribe by tribe. Then Yahweh will indicate to which tribe [the man who took those things belongs]. Then Yahweh will indicate to which clan from that tribe [the guilty man belongs]. Then Yahweh will indicate to which family he belongs. And then he will indicate which person [in that family took those things].
“‘Da safe ku zo kabila-kabila. Kabilar da Ubangiji ya ware, za tă zo gaba gida-gida; gidan da Ubangiji ya ware, za su zo gaba iyali-iyali. Iyalin kuma da Ubangiji ya ware, za su zo gaba mutum bayan mutum.
15 Then the one who has taken some of the things that should have been destroyed will be destroyed in a fire. And everything he owns will be destroyed with him, because he has disobeyed the command that Yahweh gave us and has done something that is disgraceful to us Israeli people.’”
Mutumin da aka same shi da haramtattun abubuwan kuwa za a ƙone shi, duk da mallakarsa domin ya karya sharaɗin da Ubangiji ya yi muku, ya yi abin kunya a Isra’ila!’”
16 Early the next morning, Joshua told all the Israeli people to stand before the Sacred Tent, tribe by tribe. [When they did that], Yahweh indicated that a man from the tribe of Judah [was the one who had taken the things].
Kashegari da sassafe Yoshuwa ya sa Isra’ilawa suka fito kabila-kabila, aka ware kabilar Yahuda.
17 Then the clans of Judah presented themselves, and Yahweh indicated that someone from the clan of Zerah was the guilty one. Then the families of Zerah’s clan presented themselves, and Yahweh indicated that someone from the family of Zabdi [was the guilty one].
Gidan Yahuda suka zo gaba, sai aka ware gidan Zera, aka sa suka fito iyali-iyali, sai aka ware Zabdi.
18 Then Joshua told the men from that family to present themselves. And Yahweh indicated that Achan was guilty.
Yoshuwa kuwa ya sa iyalin Zabdi suka fito mutum-mutum, sai kuwa aka ware Akan ɗan Karmi, ɗan Zimri, ɗan Zera na kabilar Yahuda.
19 Then Joshua said to Achan, “Son, tell the truth [IDM]. Confess to Yahweh, the God whom we Israelis [worship, what you have done]. And tell me what you did, and do not try to (conceal anything/prevent me from knowing what you did).”
Sai Yoshuwa ya ce wa Akan, “Ɗana, sai ka ba Ubangiji, Allah na Isra’ila ɗaukaka, ka yi masa yabo. Ka gaya mini abin da ka yi; kada ka ɓoye mini.”
20 Achan replied, “It is true. I have sinned against Yahweh, the God whom we Israelis [worship].
Akan kuwa ya amsa ya ce, “Gaskiya ne! Na yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zunubi. Ga abin da na yi.
21 Among the things [in Jericho] that I saw was a beautiful coat from Babylonia. I also saw 200 pieces of silver and some gold that weighed as much as 50 pieces of silver. I wanted those things very much for myself, so I took them. I buried them all in the ground under my tent. You will find them there. The silver is buried under the other things.”
A cikin ganimar, na ga doguwar riga mai kyau irin ta Babilon, da shekel ɗari biyu na azurfa, da kuma sandan zinariya mai nauyin shekel hamsin, sai raina ya so su, na kuwa kwashe su. Na tona rami a cikin ƙasa a tentina; na ɓoye.”
22 So Joshua sent some men [to find those things]. They ran to Achan’s tent and found all the things hidden there.
Sai Yoshuwa ya aiki’yan aika suka tafi da gudu zuwa tenti ɗin, haka kuwa suka same su a ɓoye a tentinsa, da azurfa a ƙarƙashi.
23 The men brought them all out of the tent and took them to Joshua and the rest of the Israeli people. Then they spread/laid them out on the ground, where Yahweh could see them.
Suka kwashe kayan daga tenti ɗin suka kawo wa Yoshuwa da sauran Isra’ilawa, suka baza su a gaban Ubangiji.
24 Then Joshua and the rest of the people led Achan down to the valley. They also took down there the silver, the coat, the gold, Achan’s [wife and] sons and daughters, and his cattle and donkeys and sheep, and his tent, and everything else that he owned.
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ɗauki Akan ɗan Zera, da azurfar, doguwar rigar, sandan zinariya,’ya’yansa maza da mata, shanunsa, jakuna da tumaki, tentinsa da duk abin da yake da shi, suka kai su Kwarin Akor.
25 Joshua said, “(I do not know why you caused so much trouble for us/You have caused a lot of trouble for us) [RHQ], but now Yahweh will cause trouble for you.” Then all the people threw stones at Achan and his family until they all died. Then the people burned their corpses.
Yoshuwa ya ce, “Me ya sa ka jawo mana wahala haka? Ubangiji zai kawo maka wahala kai ma a yau.” Sai dukan Isra’ilawa suka jajjefe shi, bayan da suka gama jifarsa sai suka ƙone sauran.
26 They piled rocks over [the ashes of] their [corpses], and those rocks are still there. That is why that valley is called Trouble Valley. After that, Yahweh was no longer angry [with the Israeli people].
Suka tara manyan duwatsu a kan Akan, tarin duwatsun na nan a can har wa yau. Sa’an nan Ubangiji ya huce daga fushinsa mai zafi. Saboda haka ake kiran wurin Kwarin Akor.

< Joshua 7 >