< Joshua 19 >

1 The second/next tribe that was allotted land was the tribe of Simeon. Each clan in that tribe was allotted some land that was inside the area that had been allotted to the tribe of Judah.
Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
2 Their land included the towns of Beersheba ([which is also named] Sheba), Moladah,
Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
3 Hazar-Shual, Balah, Ezem,
Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
4 Eltolad, Bethul, Hormah,
Eltolad, Betul, Horma,
5 Ziklag, Beth-Marcaboth. Hazar-Susah,
Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
6 Beth-Lebaoth, and Sharuhen. Altogether there were 13 towns and the surrounding villages.
Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
7 The land allotted to them also included the four cities of Ain, Rimmon, Ether, and Ashan, and their surrounding villages.
Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
8 They were also allotted some very small villages in an area that extended south to Baalath-Beer (which is [also named] Ramah, in the southern desert). That was the land allotted to the clans of the tribe of Simeon.
da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
9 The tribe of Judah had been allotted much more land than they needed, so part of their land was given to the tribe of Simeon.
Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
10 The third/next tribe that was allotted land was the tribe of Zebulun. Each clan of that tribe was allotted some of the land. The southern border started at Sarid [city].
Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
11 It extended west to Maralah [city] and on to Dabbesheth [city], and on to the brook just north of Jokneam [city].
Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
12 The border extended east from Sarid to the area near Kisloth-Tabor [city] and on to Daberath [town] and on to Japhia [town].
Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
13 From there it extended east to Gath-Hepher [city] and Eth-Kazin [town], and north to Rimmon [city]. From there the border extended [west] to Neah [town].
Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
14 From Neah it extended south to Hannathon [city] and from there to Iphtah-El Valley.
A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
15 Their area included the towns of Kattath, Nahalal, Shimron, Idalah, and Bethlehem. Altogether there were twelve towns and the surrounding villages.
Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
16 That was the land that was allotted to the clans of the tribe of Zebulun.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
17 The fourth/next tribe that was allotted land was the tribe of Issachar. Each of the clans of that tribe was allotted some of the land.
Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
18 Their land included the cities of Jezreel, Kesulloth, Shunem,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
19 Hapharaim, Shion, Anaharath,
Hafarayim, Anaharat,
20 Rabbith, Kishion, Ebez,
Rabbat, Kishiyon, Ebez,
21 Remeth, En-Gannim, En-Haddah, and Beth-Pazzez.
Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
22 The border of the area that was allotted to the tribe of Issachar was close to Tabor, Shahazumah, and Beth-Shemesh [cities], and ended [in the east] at the Jordan [River]. Altogether there were 16 cities and the surrounding villages.
Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
23 Those cities and villages were in the land allotted to the clans of the tribe of Issachar.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
24 The fifth/next tribe that was allotted land was the tribe of Asher. Each of the clans in that tribe was allotted some of the land.
Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
25 Their land included the towns of Helkath, Hali, Beten, Acshaph,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
26 Allammelech, Amad, and Mishal. The western border started at Carmel [Mountain] and Shihor-Libnath.
Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
27 From there it extended [southeast] to Beth-Dagon [town], and then to [the area that was allotted to the tribe of] Zebulun and Iphtah-El Valley. From there the border extended east and then north to Beth-Emek [town] and Neiel and Cabul [towns].
Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
28 From there it extended west to Abdon, Rehob, Hammon, and Kanah [cities], and continued to Sidon, which is a big city.
ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
29 From there the border extended south toward Ramah and to the big city of Tyre that had strong walls around it. From there the border extended [west] to Hosah [town] and ended at the [Mediterranean] Sea. Within their area were the towns of Aczib,
Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
30 Ummah, Aphek, and Rehob. Altogether there were 22 towns and their surrounding villages.
Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
31 Those cities and villages were within the land that was allotted to the clans of the tribe of Asher.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
32 The sixth/next tribe that was allotted land was the tribe of Naphtali. Each of the clans in that tribe was allotted some of the land.
Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
33 The border of their land started [in the west] at the [huge] oak tree at Zaanannim, near Heleph [town]. It extended [east] through Adami-Nekeb [city] and Jabneel, and then to Lakkum, and ended at the Jordan [River].
Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
34 The western boundary extended through Aznoth-Tabor as far as Hukkok [city]. It extended to the borders of [the tribe of] Zebulun at the south, to [the border of the tribe of] Asher on the west, and the Jordan [River] at the east.
Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
35 [Within their land were] several cities with strong walls around them. They were Ziddim, Zer, Hammath, Rakkath, Kinnereth,
Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
36 Adamah, Ramah, Hazor,
Adama, Rama, Hazor,
37 Kedesh, Edrei, En-Hazor,
Kedesh, Edireyi, En Hazor,
38 Iron, Migdal-El, Horem, Beth-Anath, and Beth-Shemesh. Altogether there were 19 cities and the surrounding villages.
Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
39 Those cities and surrounding villages were in the land that was allotted to the clans of the tribe of Naphtali.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
40 The seventh/last tribe that was allotted land was the tribe of Dan. Each of the clans in that tribe was allotted some of the land.
Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
41 Their land included the towns of Zorah, Eshtaol, Ir-Shemesh,
Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
42 Shaalabbin, Aijalon, Ithlah,
Shalim, Aiyalon, Itla,
43 Elon, Timnah, Ekron,
Elon, Timna, Ekron,
44 Eltekeh, Gibbethon, Baalath,
Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
45 Jehud, Bene-Berak, Gath-Rimmon,
Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
46 Me-Jarkon, Rakkon, and the area near Joppa.
Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
47 But the people of the tribe of Dan were unable to take control of the land that had been allotted to them. So they went [northeast] and fought against the people in Leshem [city]. They defeated and killed all the people who lived there. Then they began to live in Leshem, and changed the name of the city to Dan, the man from whom their tribe descended.
(Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
48 All of those towns and surrounding villages were in the land that was allotted to the clans in the tribe of Dan.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
49 After the Israeli leaders divided the land among the tribes, they allotted some land to Joshua.
Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
50 They allotted to him Timnath-Serah. Yahweh had said that he could have whatever city he wanted, and that was the city that he chose. It was in the hilly region which was allotted to the tribe of Ephraim. Joshua rebuilt the city and lived there.
yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
51 Those were the areas that were allotted to the various tribes of Israel. Eleazar the Supreme Priest and Joshua and the leaders of each tribe divided up the land while they were all at Shiloh, by (casting lots/throwing marked stones) [to decide which area each tribe would receive]. They did that while Yahweh was watching, at the entrance of the Sacred Tent. In that way they completed dividing up the land.
Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.

< Joshua 19 >