< Joshua 18 >

1 The Israeli people captured all the land [that they were able to], but there were still seven tribes that had not been allotted any land. The Israeli people all gathered at Shiloh, and they set up the Sacred Tent there.
Isra’ilawa duka suka taru a Shilo suka kafa tenti inda za su dinga taruwa. Yanzu ƙasar tana ƙarƙashin mulkinsu,
2
amma akwai sauran kabilu bakwai na Isra’ila waɗanda ba su samu rabon gādonsu ba tukuna.
3 Joshua said to them, “Why are you waiting a long time to take control of [the rest of] the land that Yahweh, the God whom your ancestors [worshiped], has promised to give to you [RHQ]?
Saboda haka Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Har yaushe za ku yi jinkirin shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji Allah na iyayenku ya ba ku?
4 Choose three men from each of your seven tribes. Then I will send them to explore [the parts of] the land [which you have not occupied yet. When they finish exploring it], they must write a report, in which they will (make a map/show the boundaries) of the land that each tribe wants to receive.
Ku ba da mutum uku daga kowace kabila, ni kuwa in aike su, su zagaya dukan ƙasar su rubuta bayani game da ita, bisa ga yadda za a raba ta gādo ga kowace kabila, sa’an nan su dawo wurina.
5 They will divide the remaining land into seven parts. The tribe of Judah will keep its land in the south, and the tribes of Ephraim and Manasseh will keep their land in the north.
Za ku raba ƙasar kashi bakwai. Mutanen Yahuda za su ci gaba da kasancewa a wurin da suke a kudu, sai kuma mutanen Yusuf a wurin da suke a arewa.
6 But in their report, the men from the seven tribes should describe the seven parts of the remaining land [that they wish to receive], and bring the report to me. While Yahweh is watching, I will (cast lots/throw marked stones) [to decide which land should be allotted to each tribe].
Bayan kun auna ƙasar, ku raba ta kashi bakwai, sai ku kawo mini taswirar ƙasar. Ni kuma in yi muku ƙuri’a a gaban Ubangiji Allahnmu.
7 But the tribe of Levi will not be allotted any land, because their [reward is that they will be] Yahweh’s priests. The tribes of Gad, Reuben, and half the tribe of Manasseh have already been allotted their land on the east side of the Jordan [River], just as Moses, the man who served God [well], decided, [so they will not get any more land].”
Lawiyawa ba su da rabo a cikinku, domin aikin firistocin da suke yi wa Ubangiji shi ne gādonsu. Gad, Ruben da rabin kabilar Manasse kuwa sun riga sun samu gādonsu a gabashin gefen Urdun, Musa bawan Ubangiji ya ba su.”
8 When the men who were chosen [got ready to] leave, Joshua told them, “Go and explore the land. Then write a report of what you have seen, and bring it back to me. Then while Yahweh is watching, I will (cast lots/throw marked stones) here at Shiloh, [to determine what area each tribe will receive].”
Da mutanen za su kama hanya su je su zāna yadda ƙasar take, Yoshuwa ya umarce su cewa, “Ku je ku ga yadda ƙasar take. Sa’an nan ku dawo wurina, zan yi muku ƙuri’a a nan Shilo a gaban Ubangiji.”
9 So the men left and walked through the area. Then they described in a scroll each town that was in the seven parts [into which they had divided] the land. Then they returned to Joshua, who was still at Shiloh.
Mutanen kuwa suka tafi suka bi ta cikin ƙasar, suka bayyana yadda take a rubuce, gari-gari, kashi bakwai, suka koma wurin Yoshuwa a Shilo.
10 [After Joshua read their report], while Yahweh was watching, he (cast lots/threw marked stones) to choose which land would be allotted to each of the seven Israeli tribes.
Sai Yoshuwa ya yi musu ƙuri’a a gaban Ubangiji, a nan ne ya raba wa Isra’ilawa ƙasar bisa ga yadda aka raba su kabila-kabila.
11 The first tribe that was allotted land was the tribe of Benjamin. Each clan in that tribe was allotted some of the land that was between the area that was allotted to the tribe of Judah and the area that was allotted to the tribes of Ephraim and Manasseh.
Ƙuri’ar kabilar Benyamin bisa ga iyalansu. Rabonsu ya kama daga ƙasar da take tsakanin kabilar Yahuda da ta Yusuf.
12 The northern border started at the Jordan [River] and extended west along the northern side of Jericho, into the hilly area. From there the border extended west to the desert near Beth-Aven [town].
Daga gefen arewa, iyakarsu ta kama ne daga Urdun, ta wuce arewa a gangaren Yeriko, ta nufi yamma cikin ƙasar kan tudu, ta fito a jejin Bet-Awen.
13 From there it extended southwest to Luz (which is [now named] Bethel). From there it extended southwest to Ataroth-Addar [town], which is on the hill south of Lower Beth-Horon [city].
Daga can ta ƙetare zuwa gangaren Luz a kudu (wato, Betel), ta wuce zuwa Atarot Adda a tudun arewa na kwarin Bet-Horon.
14 At the hill south of Beth-Horon, the border turned and extended south to Kiriath-Baal [town], which is [also named] Kiriath-Jearim. That is a town where people of the tribe of Judah live. That was the western border of the land allotted to the tribe of Benjamin.
Daga tudun da yake fuskantar Bet-Horon a kudu, iyakar ta juya kudu ta gefen yamma ta ɓullo a Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim), birnin Yahuda. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
15 The southern border of their land started near Kiriath-Jearim and extended west to Nephtoah Springs.
A gefen kudu kuwa, iyakar ta fara daga ƙauyukan Kiriyat Yeyarim wajen yamma sai ta miƙe zuwa maɓuɓɓugar ruwan Neftowa.
16 From there it extended south to the bottom of the hill, near Ben-Hinnom Valley, on the north side of Repha Valley. The border extended south along the Hinnom Valley, south of the city where the Jebus people-group lived, to En-Rogel.
Iyakar ta gangara zuwa gefen dutsen da yake fuskantar Kwarin Ben Hinnom, wanda yake arewa da Kwarin Refayim. Ta ci gaba ta gangara ta Kwarin Hinnom ta yi kudu kusa da birnin Yebusiyawa har zuwa En Rogel.
17 From there the border extended west to En-Shemesh, and continued to Geliloth near Adummim Pass. Then it extended to the great stone of Reuben’s son Bohan.
Sai ta nausa ta yi wajen arewa, zuwa En Shemesh, ta ci gaba zuwa Gelilot, wanda yake fuskantar hawan Adummim. Daga can ta gangara zuwa Dutsen Bohan, ɗan Ruben.
18 From there the border extended to the northern edge of Beth-Arabah [town] and down into the Jordan [River] Valley.
Sai ta wuce ta yi arewancin gangaren Bet-Araba, ta wuce har zuwa cikin Araba.
19 From there it extended east to the northern edge of Beth-Hoglah [town] and ended at the north end of the Dead Sea, where the Jordan [River flows into the Dead Sea]. That was the southern boundary [of the land allotted to the tribe of Benjamin].
Sa’an nan ta wuce zuwa arewancin gangaren Bet-Hogla ta kuma ɓulla a arewancin gaɓar Tekun Gishiri, a bakin Urdun a kudu. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
20 The Jordan [River] was the eastern boundary of the land allotted to the tribe of Benjamin. Those were the boundaries of the land allotted to them.
Urdun shi ne iyaka a wajen gabas. Waɗannan su ne iyakokin yankin ƙasar da iyalan kabilar Benyamin suka gāda.
21 The cities in the land allotted to the tribe of Benjamin were Jericho, Beth-Hoglah, Emek-Keziz,
Waɗannan su ne garuruwan da kabilar Benyamin suke da su na gādo. Yeriko, Bet-Hogla, Emek Keziz,
22 Beth-Arabah, Zemaraim, Bethel,
Bet-Araba, Zemarayim, Betel,
23 Avvim, Parah, Ophrah,
Awwim, Fara, Ofra,
24 Kephar-Ammoni, Ophni, and Geba. Altogether there were fourteen towns and the surrounding villages.
Kefar Ammoni, Ofni da Geba, garuruwa goma sha biyu ke nan da ƙauyukansu.
25 The tribe of Benjamin also had the towns of Gibeon, Ramah, Beeroth,
Akwai kuma Gibeyon, Rama, Beyerot,
26 Mizpah, Kephirah, Mozah,
Mizfa Kefira, Moza,
27 Rekem, Irpeel, Taralah,
Rekem, Irfeyel, Tarala,
28 Zelah, Haeleph, the city where the Jebus people-group lived (which is [now named] Jerusalem), Gibeah, and Kiriath. Altogether there were 14 towns and the surrounding villages. All that area was allotted to the clans of the tribe of Benjamin.
Zela, Hayelef, birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima), Gibeya da Kiriyat, garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu. Wannan shi ne rabon gādon kabilar Benyamin bisa ga iyalansu.

< Joshua 18 >