< Joshua 15 >

1 The land that was allotted to the tribe of Judah was divided among its clans. That land extended south along the border of the Edom region, as far as the Zin Desert.
An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
2 The southern border of the land that was allotted to the tribe of Judah started at the south end of the Dead Sea [and extended west].
Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
3 It extended south of Scorpion Pass to Zin [Desert], and from there west to a place south of Kadesh-Barnea, past Hezron [town], to Addar [town], and from there it turned [northwest] to Karka [town].
zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
4 From there it continued to Azmon, and from there to the dry riverbed on the border of Egypt, and from there [west] to the [Mediterranean] Sea. That was the southern border.
Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
5 The eastern border of the land of the tribe of Judah was the Dead Sea, and it extended [north] to [where the Jordan River ends at] the Dead Sea.
Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
6 The northern border started where the Jordan River ends at the Dead Sea. It extended [north] to Beth-Hoglah [town], and from there it extended north of Beth-Arabah [town] to the [big] stone [set up by] Reuben’s son Bohan.
wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
7 From there the border continued west through Achor Valley to Debir [city]. From there it turned north to Gilgal [city]. Gilgal is north of the road that goes through Adummim Pass, on the south side of the valley. From Gilgal the border extended west to the springs at En-Shemesh, and from there to En-Rogel.
Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
8 From there it extended through Ben-Hinnom Valley, south of the city where the Jebus people-group lived. (That city is now named Jerusalem.) From there the border extended to the top of the hill on the west side of Hinnom Valley, at the northern end of the valley where the Repha [giants] lived.
Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
9 From there the border extended [northwest] to Nephtoah Spring, and from there to the cities near Ephron Mountain. From there the border extended [west] toward Baalah, which is now named Kiriath-Jearim.
Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
10 Then the border extended further west to Seir Mountain. Then it continued [southwest] along the north side of Jearim Mountain, which is also named Kesalon, to Beth-Shemesh [city]. From there it extended [northwest] past Timnah [city],
Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
11 to the hill north of Ekron [city]. From there it extended [west] to Shikkeron [town] and past Baalah Mountain to Jabneel [town], then [northwest] to the [Mediterranean] Sea.
Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
12 The western border of the land that was allotted to the tribe of Judah was the Mediterranean Sea. All the clans of Judah lived inside those borders.
Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
13 Yahweh commanded Joshua to give part of the land for the tribe of Judah to Caleb. So he gave to Caleb Kiriath-Arba [city], which is now named Hebron. (Arba was the ancestor of the Anak people-group.)
Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
14 Caleb forced the three clans of the Anak people-group to leave Hebron. Those were the Sheshai, Ahiman, and Talmai clans.
Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
15 Then Caleb left there and went to fight against the people living in Debir [city], which was previously named Kiriath-Sepher.
Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
16 Caleb said, “If someone attacks [the people in] Kiriath-Sepher and captures their city, I will give my daughter Acsah to him to be his wife.”
Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
17 Othniel, the son of Caleb’s brother Kenaz, captured the city. So Caleb gave his daughter to him.
Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
18 When Caleb’s daughter married Othniel, she told him to ask her father to give her a field. Then Acsah went to talk with her father Caleb. As she got down from her donkey, Caleb asked her, “Do you want something?”
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
19 Acsah replied, “Yes, I want you to do something for me. You have given me some land in the southern part of Canaan, [but there is no water there]. So please give me some [land that has] springs.” So Caleb gave her the upper and lower springs [near Hebron].
Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
20 [Here is a list of the towns in] the land [that God had promised to] give to the tribe of Judah. Each clan was allotted some of the land.
Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
21 The tribe of Judah was allotted all these towns in the southern [desert area of Canaan], near the border of the Edom [region]: Kabzeel, Eder, Jagur,
Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
22 Kinah, Dimonah, Adadah,
Kina, Dimona, Adada,
23 Kedesh, Hazor, Ithnan,
Kedesh, Hazor, Itnan,
24 Ziph, Telem, Bealoth,
Zif, Telem, Beyalot,
25 Hazor-Hadattah, Kerioth-Hezron (which is also named Hazor),
Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
26 Amam, Shema, Molodah,
Amam, Shema, Molada,
27 Hazar-Gaddah, Heshmon, Beth-Pelet,
Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
28 Hazar-Shual, Beersheba, Biziothiah,
Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
29 Baalah, Iim, Ezem,
Ba’ala, Iyim, Ezem,
30 Eltolad, Kesil, Hormah,
Eltolad, Kesil, Horma,
31 Ziklag, Madmannah, Sansannah,
Ziklag, Madmanna, Sansanna,
32 Lebaoth, Shilhim, Ain, and Rimmon. There were 29 towns altogether and their surrounding villages.
Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
33 The tribe of Judah was allotted these towns in the [northern part of the western] foothills: Eshtaol, Zorah, Ashnah,
Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
34 Zanoah, En-Gannim, Tappuah, Enam,
Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
35 Jarmuth, Adullam, Socoh, Azekah,
Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
36 Shaaraim, Adithaim, and Gederah (which is also named Gederothaim). Altogether there were 14 towns and their surrounding villages.
Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
37 [The tribe of Judah was also allotted these towns in the southern part of the western foothills]: Zenan, Hadashah, Migdal-Gad,
Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
38 Dilean, Mizpah, Joktheel,
Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
39 Lachish, Bozkath, Eglon,
Lakish, Bozkat, Eglon,
40 Cabbon, Lahmas, Kitlish,
Kabbon, Lahman, Kitlish,
41 Gederoth, Beth-Dagon, Naamah, and Makkedah. There were 16 towns altogether and their surrounding villages.
Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
42 The tribe of Judah was also allotted these towns in [the central part of] the western foothills: Libnah, Ether, Ashan,
Libna, Eter, Ashan,
43 Iphtah, Ashnah, Nezib,
Yefta, Ashna, Nezib,
44 Keilah, Aczib, and Mareshah. There were nine towns altogether, with their surrounding villages.
Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
45 The tribe of Judah was also allotted these towns [close to the Mediterranean Sea] with their surrounding villages: Ekron and the towns between Ekron and the coast, Ashdod, and Gaza. The area extended south to the dry riverbed on the border of Egypt.
Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
48 The tribe of Judah was also allotted these towns in [the southwest part of] the hilly region: Shamir, Jattir, Socoh,
Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
49 Dannah, Kiriath-Sannah (which is now named Debir),
Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
50 Anab, Eshtemoh, Anim,
Anab, Eshtemo, Anim,
51 Goshen, Holon, and Giloh. There were eleven towns with their surrounding villages.
Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
52 The tribe of Judah was also allotted these towns in [the south-central part of] the hilly region: Arab, Dumah, Eshan,
Arab, Duma, Eshan,
53 Janim, Beth-Tappuah, Aphekah,
Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
54 Humtah, Kiriath-Arba (which is now named Hebron), and Zior. There were nine towns altogether with their surrounding villages.
Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
55 The tribe of Judah was also allotted these towns [in the southeastern part of the hilly region]: Maon, Carmel, Ziph, Juttah,
Mawon, Karmel, Zif, Yutta
56 Jezreel, Jokdeam, Zanoah,
Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
57 Kain, Gibeah, and Timnah. There were ten towns altogether with their surrounding villages.
Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
58 The tribe of Judah was also allotted these towns [in the central part of the hilly region]: Halhul, Beth-Zur, Gedor,
Halhul, Bet-Zur, Gedor,
59 Maarath, Beth-Anoth, and Eltekon. There were six towns altogether with their surrounding villages.
Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
60 The tribe of Judah was also allotted two towns [in the northern part of the hilly region], Rabbah and Kiriath-Baal (which is also named Kiriath-Jearim).
Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
61 The tribe of Judah was also [allotted these towns] in the desert [near the Dead Sea]: Beth-Arabah, Middin, Secacah,
Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
62 Nibshan, Salt city, and En-Gedi. There were six towns altogether with their surrounding villages.
Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
63 [The army of the tribe of] Judah was not able to force the people of the Jebus people-group to leave Jerusalem. So the people of that group are still living among the tribe of Judah.
Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.

< Joshua 15 >