< Joshua 10 >

1 Later, Adonizedek, the king of Jerusalem, heard that Joshua’s army had captured Ai [town] and had destroyed everything in the town. He heard that they had done to the people of Ai and to their king the same thing that they had done to the people of Jericho and their king. He also heard that the people of Gibeon [city] had made a peace treaty with the Israeli people, and that the people of Gibeon were now living near the Israelis and being protected by them.
Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya ji cewa Yoshuwa ya ci Ai da yaƙi ya kuma hallaka ta sarai, ya yi wa Ai da sarkinta abin da ya yi wa Yeriko da sarkinta, mutanen Gibeyon kuwa sun yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, suna kuma zama kusa da su.
2 Because of that, he and the people whom he ruled became very afraid, because Gibeon was an important city, like the other cities that had kings. And [even though] Gibeon was a larger city than Ai and all its soldiers were good fighters, [they thought Joshua’s army might defeat them].
Shi da mutanensa suka ji tsoron wannan sosai, gama Gibeyon muhimmiyar birni ce, har ma kamar ɗaya daga cikin biranen sarauta, ya ma fi Ai girma, mazanta duka kuwa mayaƙa ne na ƙwarai.
3 So King Adonizedek sent a message to Hosham the king of Hebron [city], to Piram the king of Jarmuth [city], to Jarmuth the king of Lachish [city], and to Debir the king of Eglon [city].
Saboda haka sai Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya roƙi Hoham sarkin Hebron, Firam sarkin Yarmut, Yafiya sarkin Lakish da Debir sarki Eglon ya ce,
4 In the message he said, “Please come up with your armies and help me to attack Gibeon, because the people of Gibeon have made a peace treaty with Joshua and the Israelis.”
“Ku zo ku taimake ni in kai wa Gibeyon hari. Domin sun yi yarjejjeniya ta salama da Yoshuwa da Isra’ilawa.”
5 So those five kings who ruled all the groups who were descendants of Amor—the kings of Jerusalem, Hebron, Jarmuth, Lachish, and Debir—came up with all of their soldiers and surrounded the city. Then they prepared to attack it.
Sai sarakunan nan biyar na Amoriyawa, sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon suka haɗa sojojinsu. Suka je dukansu suka yi shirin kai wa Gibeyon hari.
6 So the people of Gibeon sent a message to Joshua while he was in the camp at Gilgal. They said, “We are your servants. So do not forsake us. Come up to us quickly and save us! Help us, because the kings of all of the groups descended from Amor and their armies have joined their forces and have come from the hilly area to attack us!”
Sai mutanen Gibeyon suka aika zuwa wurin Yoshuwa a sansani a Gilgal, “Kada ka juya wa bayinka baya, ka zo da sauri ka cece mu! Ka taimake mu domin sarakunan Amoriyawa duka daga kan tudu sun haɗa ƙarfinsu tare za su tasar mana.”
7 So Joshua and all his army, including the soldiers who were his best fighting men, marched up from Gilgal.
Saboda haka Yoshuwa ya tashi da rundunarsa duka, tare da dukan jarumawansa.
8 Then Yahweh said to Joshua, “Do not be afraid of those armies! I will enable your army to defeat them [IDM]. None of them will be able to (resist/fight and defeat) your army.”
Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu; na ba ka su a hannunka. Ba waninsu da zai iya tsayayya da kai.”
9 Joshua’s army marched all night and arrived very early in the morning.
Bayan sun yi tafiya dukan dare daga Gilgal, Yoshuwa ya auko musu ba labari.
10 They attacked their enemies before anyone knew that they had come. Yahweh caused their enemies to (become very confused/start running in all directions) when they saw the Israeli army. As a result, the Israeli army defeated them very severely at Gibeon [and killed many of them]. The rest of them fled along the road that goes up to Beth-Horon. But the Israeli army pursued them and killed them all along the road that goes to Azekah and Makkedah towns.
Ubangiji ya sa suka ruɗe a gaban Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka yi babbar nasara a kansu a Gibeyon. Isra’ilawa suka fafare su a kan hanyar zuwa Bet-Horon suka karkashe su duka har zuwa Azeka da Makkeda.
11 As they fled in front of the Israeli army, Yahweh threw down huge hailstones from the sky. As a result, more of them died from hailstones falling on them than died as a result of the Israeli army killing them with swords.
Suna guje wa Isra’ilawa suna gangarawa a kan hanyar Bet-Horon har zuwa Azeka, sai Ubangiji ya turo manyan duwatsu daga sararin sama suka karkashe su, waɗanda manyan duwatsun suka kashe sun fi waɗanda Isra’ilawa suka kashe da takobi.
12 On the day that Yahweh enabled the Israeli army to defeat the groups who were descendants of Amor, Joshua said to Yahweh while the Israeli people were listening, “Yahweh, cause the sun to stand still over Gibeon, and cause the moon to not move when it is over Aijalon Valley.”
A ranar da Ubangiji ya ba da Amoriyawa a hannun Isra’ilawa, Yoshuwa ya ce wa Ubangiji a gaban Isra’ilawa, “Ke rana, ki tsaya cik a Gibeyon Kai wata, ka je Kwarin Aiyalon.”
13 And that is what happened. The sun stood still, and the moon did not move, until the Israeli army defeated their enemies. That is what has been written in the book that Jashar wrote. The sun stopped while it was in the middle of the sky, and did not (set/go down) for about a whole day.
Sai rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya, har sai da al’ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gābanta, kamar yadda aka rubuta a cikin littafin Yashar. Rana ta tsaya a sararin sama, ba tă fāɗi ba har kusan yini guda.
14 On that day Yahweh did a great miracle that someone asked him to do. There was never a day like that previously, and there has never been a day like that since. Yahweh was certainly fighting for the Israeli people!
Ba a taɓa ganin abu haka ba ko dā can, ranar da Ubangiji ya saurari mutum. Ba shakka Ubangiji yana yaƙi domin Isra’ilawa.
15 After Joshua’s army defeated their enemies, they all returned to their camp at Gilgal.
Sai Yoshuwa ya koma sansanin Gilgal tare da dukan Isra’ilawa.
16 While the enemy soldiers were fleeing from Joshua’s army, their five kings also fled and hid in a cave at Makkedah [town].
Sarakunan guda biyar suka gudu, suka ɓuya a cikin kogo a Makkeda.
17 Then someone told Joshua, “We found those five kings, hiding in a cave at Makkedah!”
Lokacin da aka gaya wa Yoshuwa cewa an sami sarakunan nan biyar a ɓoye a cikin kogo a Makkeda.
18 When Joshua heard that, he said, “Roll some very large rocks to the entrance of the cave so that the kings cannot escape, and leave some soldiers there to guard it.
Sai ya ce, “Ku mirgina manyan duwatsu ku rufe bakin kogon, sai ku sa waɗannan mutane su yi tsaron kogon.
19 But do not stay there! Pursue our enemies! Attack them from behind! Do not allow them to escape to their cities, because Yahweh, our God, will enable you to defeat/kill them. [IDM]”
Amma kada ku tsaya a can! Ku fafari abokan gābanku, ku kai musu hari ta baya, kada ku bari su kai biranensu, gama Ubangiji Allahnku ya ba da su a hannunku.”
20 So Joshua’s army did what he told them to do. They killed almost all of the enemy soldiers, but a few of them were able to reach their cities and be safe inside the walls of the cities.
Saboda haka Yoshuwa da Isra’ilawa suka hallaka su da yawa ƙwarai, amma’yan kaɗan ɗin da suka rage suka tsere zuwa cikin biranensu masu kāriya.
21 Then Joshua’s army returned to Joshua, who was still in their camp at Makkedah. No one in the land dared to criticize [MTY] the Israelis.
Dukan rundunar kuma suka dawo sansanin Makkeda tare da Yoshuwa, ba abin da ya same su. Ba wanda ya sāke tsokanar Isra’ilawa.
22 Then Joshua said, “Open the entrance of the cave, and bring out to me those five kings!”
Yoshuwa ya ce, “Ku buɗe bakin kogon ku kawo mini sarakunan nan guda biyar.”
23 So the soldiers brought those five kings out of the cave—the kings of Jerusalem, Hebron, Jarmuth, Lachish, and Eglon.
Sai suka kawo sarakunan biyar daga cikin kogo; sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon.
24 When they brought those kings to Joshua [and forced them to lie on the ground], he summoned all the Israeli soldiers, and then he said to the army commanders, “Come here and put your feet on the necks of these kings!” So the commanders did that.
Sa’ad da aka kawo sarakunan nan wurin Yoshuwa, ya kira dukan Isra’ilawa ya ce wa shugabannin rundunoni waɗanda suke tare da shi, “Ku zo nan ku taka wuyan sarakunan nan.” Sai suka zo suka taka wuyansu.
25 Then Joshua said to them, “Do not be afraid of any of our enemies! Never be discouraged! Be strong and courageous. This is what Yahweh will do to all the enemies you will fight!”
Yoshuwa ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ko kuwa ku razana, amma ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Haka Ubangiji zai yi da duk abokan gāban da za ku yi yaƙi da su.”
26 Then Joshua killed each of the five kings with his sword, and told his soldiers to hang the bodies of the five kings on trees. So they did that, and they left the bodies hanging on the trees until sunset.
Sai Yoshuwa ya karkashe waɗannan sarakuna guda biyar, ya kuma rataye kowannensu a bisa itace inda jikunansu suka kasance har yamma.
27 At sunset, Joshua told them to take the bodies down from the trees and throw them into the cave where they had been hiding. So the soldiers did that, and then they put those large rocks at the entrance of the cave again. Those rocks are still there.
Da yamma Yoshuwa ya ba da umarni a sauko da su daga itatuwan a jefa su cikin kogon da suka ɓuya. Aka sa manyan duwatsu aka rufe bakin kogon, suna a can har wa yau.
28 That is how Joshua’s army attacked and captured Makkedah. They killed the king and everyone else in the town. They did not leave anyone alive. They did to the king of Makkedah the same thing that they had done to the king of Jericho.
A ranan nan Yoshuwa ya ci Makkeda da yaƙi. Ya karkashe mutanen tare da sarkinta. Bai bar wani da rai ba. Ya yi wa sarkin Makkeda yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
29 That same day, Joshua and his Israeli army went [southwest] from Makkedah to Libnah [city] and attacked it.
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Makkeda zuwa Libna, suka kai mata hari.
30 Yahweh enabled the Israelis to conquer [MTY] that city and its king. They killed everyone in the city; they did not (spare anyone/allow anyone to remain alive). They killed the king of Libnah just like they had killed the king of Jericho.
Ubangiji kuma ya ba da ƙasar da sarkinta a hannun Yoshuwa. Yoshuwa ya karkashe kowa ya hallaka birnin, bai bar wani da rai ba. Ya kuma yi wa sarkin yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
31 Then Joshua and his army went [south] from Libnah to Lachish [city]. They surrounded the city and attacked it.
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Libna zuwa Lakish; suka yi shiri suka kai mata hari.
32 On the second day of the battle, Yahweh enabled the Israelis to conquer [MTY] the city. And like they had done at Libnah, they killed everyone [DOU] in the city.
Ubangiji ya ba da Lakish a hannun Isra’ilawa, a rana ta biyu kuwa Yoshuwa ya ci nasara a kansu. Ya karkashe duk mutanen birnin ya kuma hallaka birnin, kamar yadda ya yi a Libna.
33 King Horam from Gezer [city and his army] came to help [the soldiers of] Lachish, but Joshua’s [army] defeated Horam and his army, and did not allow any of them to remain alive.
Horam sarkin Gezer kuwa ya zo don yă taimaki Lakish, amma Yoshuwa ya haɗa duk da shi da rundunarsa ya ci su da yaƙi, har bai bar waninsu da rai ba.
34 Then Joshua and his army went [west] from Lachish to Eglon [city]. They surrounded the city and attacked it.
Yoshuwa kuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Lakish zuwa Eglon; suka yi shiri suka kai mata hari.
35 On that day, they captured the city and killed [MTY] everyone in it [DOU], just like they had done at Lachish.
A ranan nan suka ci ƙasar da yaƙi, suka buge ta, suka karkashe kowa da takobi kamar dai yadda suka yi a Lakish.
36 Then Joshua and his army went [west from Eglon] up [into the hills] to Hebron [city]. They attacked the city
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Eglon zuwa Hebron suka kai hari a can.
37 and captured it. They killed the king and everyone else, just like they had done at Eglon. They did not allow anyone to remain alive.
Suka ci birnin da yaƙi, suka karkashe mazaunanta, da sarkin, har da ƙauyukan, ba wanda ya tsira kamar yadda ya yi wa Eglon. Ya hallakar da ita sarai duk da kowane mutum da yake cikinta.
38 Then Joshua and his army turned [south] and went to Debir [city] and attacked it.
Yoshuwa da Isra’ilawa duka suka juya suka kai wa Debir hari,
39 They captured the city and its king, and also captured the nearby towns. Then they killed everyone [DOU]; they did to the people there the same thing that they had done at Hebron and Libnah.
suka hallaka birnin, da sarkinta da ƙauyukanta, suka karkashe dukan mazaunan wurin, ba su bar wani da rai ba. Suka yi wa Debir da sarkinta yadda suka yi wa Libna da sarkinta da kuma Hebron.
40 That is how Joshua [and his army] conquered the entire southern part of Canaan. They defeated the kings [who ruled] the hilly area, the dry southern area, the [western] foothills, and the [eastern] slopes. They killed everyone [DOU] in those areas; they did not allow anyone to remain alive.
Yoshuwa ya cinye yankin duka da yaƙi, haɗe da na kan tudu, da Negeb, da kwarin yamma, da filayen cikin duwatsu tare da sarakunansu duka. Bai bar wani da rai ba, ya kashe duk wani mai numfashi, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ilawa ya umarta.
41 Joshua’s soldiers captured all the cities from Kadesh-Barnea [city] in the far south to Gaza [city] near the coast, including all the Goshen area, and north to Gibeon [city].
Yoshuwa ya ci su da yaƙi daga Kadesh Barneya zuwa Gaza, da kuma daga dukan yankin Goshen zuwa Gibeyon.
42 At that one time, Joshua’s army conquered all the kings and captured all the territory that they [ruled]. They were able to do that because Yahweh, the God whom the Israeli people [worship], was fighting for them.
Yoshuwa kuwa ya cinye sarakunan nan duka da ƙasashensu gaba ɗaya gama Ubangiji, Allah na Isra’ila ne ya yi yaƙi domin Isra’ilawa.
43 Then Joshua and his army returned to their camp at Gilgal.
Yoshuwa kuwa ya dawo da dukan Isra’ilawa zuwa sansani a Gilgal.

< Joshua 10 >