< Jonah 4 >

1 But Jonah was very distressed [that God had not destroyed Nineveh]. He became very angry. [The people of Nineveh were non-Jews, and Jonah did not think that God should act mercifully toward anyone who was not a Jew].
Sai abin ya ɓata wa Yunana rai ƙwarai har ya yi fushi.
2 He prayed to Yahweh, “O Yahweh, what you have done is what I thought that you would do, before I left home [RHQ]. That is why I [decided] immediately to run away, and go to Tarshish [city], because I knew that you, O God, act very kindly and compassionately [toward all people]. You do not quickly become angry with people who do evil things. You love people very much, and you change your mind about punishing [people who sin].
Sai ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ba irin abin da na faɗa ke nan ba tun ina gida? Wannan ne ya sa na yi ƙoƙarin tserewa zuwa Tarshish. Ai, na sani kai Allah ne mai alheri da tausayi, mai jinkirin fushi da cikakkiyar ƙauna, kai Allah ne mai dakatar da nufinka na yin hukunci.
3 [So] now, O Yahweh, [since you will not destroy Nineveh city as you said you would], allow me to die, because it would be better for me to die than to [continue to] live.”
Yanzu, ya Ubangiji, ka ɗauki raina, domin ya fi sauƙi a gare ni in mutu da in rayu.”
4 Yahweh replied, “(Why is it right for you to be angry [about my not destroying the city]?/It is not right for you to be angry [about my not destroying the city]!) [RHQ]”
Amma Ubangiji ya amsa, ya ce; “Daidai ne ka yi fushi?”
5 Jonah [did not reply]. He went out of the city to the east [side of it]. He made a small shelter in order that he could sit under it and be protected from the sun. He sat under the shelter and waited to see what would happen to the city.
Sai Yunana ya fita daga birnin ya yi wajen gabas, ya zauna. A nan ya yi wa kansa rumfa, ya zauna cikin inuwarta yana jira yă ga abin da zai sami birnin.
6 Then Yahweh God caused a vine to grow up [immediately] to shade Jonah’s head from the sun and make him [feel] more comfortable. Jonah was very happy about [having] the vine [over his head].
Sai Ubangiji Allah ya sa wata’yar kuringa ta tsiro, ta yi girma a inda Yunana yake, don ta inuwantar da shi, yă ji daɗi. Yunana kuwa ya yi murna matuƙa da wannan kuringa.
7 But before dawn the next day, God sent a worm that chewed the vine, with the result that the vine withered.
Amma kashegari da safe sai Allah ya sa tsutsa ta cinye’yar kuringar har ta mutu.
8 Then, when the sun rose [high in the sky], God sent a very hot wind from the east, and the sun shone very strongly on Jonah’s head, with the result that he felt faint. He wanted to die, and he said, “It would be better for me to die than to [continue to] live!”
Sa’ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro, zafin ranar kuma ya buga kan Yunana, har ya ji sai ka ce zai suma. Ya so a ce ya mutu ma, sai ya ce, “Gara in mutu da a ce ina zaune da rai.”
9 But God asked Jonah, “Is it right for you to be angry about [what happened to] the vine?” Jonah replied, “[Yes], it is right! [Now] I am very angry and I want to die!”
Amma Allah ya ce wa Yunana, “Daidai ne ka yi fushi saboda wannan kuringa?” Sai Yunana ya ce, “I, daidai ne, ina fushi matuƙa, har ina so da na mutu ma.”
10 But Yahweh said [to him], “You have been concerned about my [causing] that vine [to wither], even though you did not take care of it, and you did not make it grow. It just grew up during one night, and it completely withered [at the end of] the next night.
Sai Ubangiji ya ce, “Ai, wannan kuringa ta tsira dare ɗaya ta kuma ɓace kafin dare na biyu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓace saboda ita.
11 But there are more than 120,000 people in Nineveh who [are very young, and because of that], they cannot tell which is their right hand and which is their left hand, and there are also many cattle, [and none of these have done anything to displease me]. So (is it not right for me to be concerned about the people of that huge city, [and not want to destroy them]?/it is certainly right for me to be concerned about the people of that huge city [and not want to destroy them]!) [RHQ]”
Ashe, ba dole ne in ji tausayin babban birnin nan Ninebe mai mutum sama da dubu ɗari da ashirin marasa alhaki, da kuma dabbobi masu yawa ba?”

< Jonah 4 >