< John 9 >

1 As Jesus walked along [with us], he saw a man who had been blind from the time he was born.
Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa.
2 We disciples asked him, “Teacher, was this man blind from when he was born because his parents sinned or because he himself sinned?”
Sai almajiransa suka tambaye shi, “Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?”
3 Jesus replied, “His being blind was not because he or his parents sinned. Instead, [he has been blind] in order that [people can] see the power of God {the power of God can be seen} as a result of [what will now happen] to him.
Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa.
4 While there is still time, I must do the work that the one who sent me [wants me to do. Just like daytime is followed by] nighttime when people do not work, [at the end of our lives] [MET] [it is too late for us to do what God wants].
Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki.
5 While I am still [living] in this world, I am the [one who enables people to know about God, like] [MET] [a] light enables the people in [MTY] this world [to see what is in the darkness].”
Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya.”
6 After he said that, he spat on the ground. He made [a little bit of] mud with the saliva, and put it on the man’s eyes.
Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
7 Then he said to him, “Go and wash in Siloam pool!” (That name means ‘sent;’ [just like they sent the water by a channel into the pool, God sent Jesus]). So the man went and washed [in the pool], and when he went home he was able to see!
Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
8 His neighbors and others who previously had seen him when he was begging said, “He is the man who used to sit here and beg, isn’t he?”
Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
9 Some said, “[Yes], he is.” Others said, “No, [he is not]. It is [just] a man who looks like him!” But the man himself said, “Yes, I am that man!”
Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
10 So they said to him, “How is it that now you can see?”
Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
11 He replied, “The man whose name is Jesus made some mud and put it on my eyes. Then he told me to go to Siloam [pool] and wash. So I went there and washed, and then I could see.”
Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
12 They said to him, “Where is that man [now]?” He said, “I do not know.”
Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
13 They took to the Pharisees the man who was previously blind.
Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
14 The day on which Jesus made the mud and enabled the man to see again was a (Sabbath/Jewish day of rest). [The Pharisees considered that healing someone was work, and their rules did not permit people to do any work] ([on the Sabbath/on the Jewish rest day]).
A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.
15 So the Pharisees also asked that man, “How did you become able to see?” He said to them, “The man put mud on my eyes. Then I washed, and now I can see!”
Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, “Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani.”
16 So some of the Pharisees said, “Since this man [Jesus] disobeys [our rules about working] (on the Sabbath/on the Jewish rest day), he is not from God.” But others said, “If he was a sinner, (he could certainly not do such miracles!/how could he do such miracles?) [RHQ]” So they were divided.
Wadansu daga cikin farisawa suka ce, “Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. “Wadansu suka ce, “Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?” Sai rabuwa ta shiga tsakanin su.
17 So one of them said to the blind man again, “You are the man whom he enabled to see. What do you yourself say about him?” The man said, “[I think] he is a prophet!” [So they told him to go].
Sai suka tambayi makahon kuma, “Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?” Makahon ya ce, “shi annabi ne.”
18 The Jewish [leaders] [SYN] still did not believe that the man was blind when he was born, and that he was [now] able to see. So they sent someone to bring the man’s parents.
Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.
19 [When they got there], one of [the Jewish leaders] asked them, “Is that man your son? Do you say that he was blind when he was born? [If that is true], how is he now able to see?”
Su ka tambayi iyayen, “Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?”
20 His parents replied, “We know that he is our son. We know that he was blind when he was born.
Sai iyayen suka amsa masu, “Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi.
21 But we do not know how he is able to see now. We also do not know who enabled him to see. Ask our son! He is old enough [to answer questions from authorities like you] He can tell you himself!”
Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa.”
22 The Jewish [leaders] [SYN] had previously declared that they would prevent anyone who declared that Jesus was the Messiah from [entering] their synagogues. His parents [knew that, so] they were afraid of the Jewish [leaders] [SYN].
Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a.
23 That is the reason that they said, “He is old enough [to answer questions], so ask him!”
Domin wannan ne, iyayensa suka ce, “Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
24 So they sent someone to bring back to them the man who had been blind. [When he got there], the [Jewish leaders] said to him, “Knowing that God [is listening] [IDM], tell the truth! We know that the man who healed you is a sinner.”
Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, “Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne.”
25 He replied, “I do not know if he is a sinner or not. But one thing I do know is that I was blind, but now I can see!”
Sai wannan mutum ya amsa, “Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani.”
26 So they said to him, “What did he do to you? How did he enable you to see?”
Sai su ka ce masa, “Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?”
27 He replied, “I told you that already, but you did not [RHQ] pay attention! Why do you want to hear me tell you again? (Do you also want to become his disciples?/You talk as though [IRO] you also want to become his disciples [RHQ]).”
Ya amsa, “Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
28 Then they insulted him angrily. They said, “You are that man’s disciple, but we are Moses’ disciples!
Sai suka kwabe shi suka ce, “kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne.
29 We know that God spoke to Moses; but this man, we do not know where he is from or where he [gets any authority] from!”
Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba.”
30 The man replied, “That is very surprising! You [say that] you do not know where he [gets any authority]. But he enabled me to see!
Mutumin ya amsa masu ya ce, “Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu.
31 We know that God does not help sinners [who ask God to help them]. Instead, he listens to [and helps] godly people who pray. He listens to people who do what God wants.
Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
32 No one has ever enabled a man to see who was blind when he was born [like I was]. That has never happened since the world began! (aiōn g165)
Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. (aiōn g165)
33 So if this man had not come from God, he would not be able to do anything [like that]!”
In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
34 They replied to him, “You (were born [as a result of your parents’] sin [EUP]/bastard)! (Do you think you are qualified to teach us?/You are not qualified to teach us!) [RHQ]” Then they threw him out [of the synagogue].
Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
35 Jesus heard [people say] that they had thrown that man out. He found the man and said to him, “Do you believe that the one who came down from heaven [is the Messiah]?”
Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
36 The man answered, “Sir, who is he? [Tell me], in order that I may believe in him.”
Sai ya amsa masa yace, “Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?”
37 Jesus said to him, “You have seen him. [In fact, it is I], the one who am speaking to you.”
Yesu yace masa, “Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai.”
38 The man said, “Lord, I believe that [you are the Messiah]!” Then he [knelt down before] Jesus and worshipped him.
Mutumin ya ce, “Ubangiji, Na bada gaskiya.” Sai ya yi masa sujada.
39 Jesus said, “I have come into this world to judge [the people in the world]. The result will be that [those who realize that they do not know God’s truth will perceive it. That is like] [MET] [enabling] those who are blind to see. But the result will also be that people who [falsely think] [IRO] that [they understand God’s truth will never understand it. That is like] [MET] [people] who are blind remaining blind permanently.”
Yesu ya ce, “Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi.”
40 Some of the Pharisees who were with him heard him say that, and said to him, “You are not suggesting that we are [like] blind people, are you?”
Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, “Muma makafi ne?”
41 Jesus said to them, “If you [realized that you did not yet know God’s truth, but you wanted to, then you would be like] blind people [who wanted to see. God would be able to] forgive your sins. But you are now [falsely] claiming that you [know God’s truth, so you are like people who are blind who claim that they] can see. [Because of that, God is not able to] forgive your sins.”
Yesu ya ce masu, “Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.

< John 9 >