< John 18 >
1 After Jesus finished praying, he went across the Kidron Brook, along with [us] disciples, to a grove [of olive trees].
Bayan Yesu ya fadi wadannan maganganu, ya fita shi da almajiransa zuwa daya barayin kwarin Kidiron, inda wani lambu ya ke, ya kuma shiga da almajiransa.
2 Judas, who was [about to] enable Jesus’ enemies to seize him, knew that [he would probably be] there. [He knew that because] Jesus often gathered there with us.
Yahuza ma wanda zai bashe shi ya san wurin, domin Yesu ya saba zuwa wurin da almajiransa.
3 So Judas came to that grove. He was leading a troop of Roman [soldiers] and some Temple guards who had been sent by the Pharisees and chief priests. They were carrying torches and lamps and weapons.
Yahuza kuwa, bayan ya dauko kungiyar soja daga manyan firistoci, da Farisawa, da 'yan majalisa, suka zo wurin, rike da fitilu, da cociloli, da makamai.
4 Jesus knew everything that was about to happen to him. So [as they approached], he stepped forward and asked them, “Who are you looking for?”
Sai Yesu, da ya san duk abinda ke faruwa da shi, yayiwo gaba, yace masu, ''Wa kuke nema''
5 They replied to him, “Jesus, the man from Nazareth.” He replied, “That is who I am.” Judas, the one who was enabling his enemies to seize him, was with them.
Suka amsa masa su ka ce, ''Yesu Banazare'' Yesu yace masu, Ni ne'' Yahuza kuma, wanda ya bashe shi, yana tsaye tare da sojojin.
6 When Jesus told them, “That is who I am,” they lurched backward and fell down on the ground [because of his power].
Sa'adda ya ce masu, ''Ni ne'', suka koma da baya, suka fadi a kasa.
7 He asked them again, “Who are you looking for?” They said, “Jesus, [the man] from Nazareth.”
Ya sake tambayarsu kuma, ''Wa ku ke nema?'' su ka ce, ''Yesu Banazare.''
8 Jesus replied, “I told you that I am Jesus. So since I am the one you are looking for, allow these [disciples of mine] to go.”
Yesu ya amsa, ''Ai, na gaya maku cewa, Ni ne. In kuwa ni ku ke nema, ku bar wadannan su tafi abinsu;''
9 [This happened] in order that [when they did what he asked them to do], the words would be fulfilled that he had prayed, “I will never lose any of those whom God has brought to me.”
Wannan kuwa domin maganar daya fada ta cika, ''Daga cikin wadanda ka ba ni, ko daya bai bace mani ba.''
10 Simon Peter had a [long] dagger. So he drew it and [tried to kill] the high priest’s servant, [but he only] cut off the man’s right ear. The servant’s name was Malchus.
Saminu Bitrus kuwa, da ya ke yana da takobi, ya zaro ya kai wa bawan babban firist sara, ya dauke masa kunnensa na dama, sunan bawan Malkus ne.
11 Jesus said to Peter, “Put your sword [back] into its sheath! (I must endure what [my] Father wants me to suffer./Do you not think that I must endure what [my] Father wants me to suffer?) [MET, RHQ]”
Yesu ya ce wa Bitrus, ''Mai da takobin ka kubenta. Ba zan sha kokon da Uba ya ba ni ba.'?
12 Then the troop of soldiers, along with their commander and the Jewish Temple guards, seized Jesus. They tied his hands [behind his back].
Sai sojojin da hafsan, da 'yan majalisar Yahudawa, suka kama Yesu, suka daure shi.
13 Then they took him first to Annas, [who was previously the high priest]. He was the father-in-law of Caiaphas. Caiaphas was the high priest that year.
Da fari suka tafi da shi wurin Hanana, don shi surukin Kayafa ne, wanda ya ke shi ne babban firist a shekaran nan.
14 Caiaphas was the one who [previously] advised the Jewish [Council] that it would be better if one man died for the sake of the people [than for all the people of the Jewish nation to die].
Kayafa kuma shi ne ya ba Yahudawa shawara, cewa ya fiye masu mutum daya ya mutu domin mutane.
15 Simon Peter and [I] were following Jesus. Because the high priest knew [me], [his doorkeeper permitted me] to enter the courtyard.
Saminu bitrus ya bi bayan Yesu, haka kuma wani almajirin yayi. Almajirin nan kuwa sananne ne ga babban firist, sai ya shiga har farfajiyar babban firist din tara da Yesu;
16 But Peter [had to] wait outside near the doorway. However, since I knew the high priest, I went back to the doorway and spoke to the girl who was guarding the entrance. Then [she allowed] Peter to come in.
Amma bitrus kuwa ya tsaya a bakin kofa daga waje. Sai daya almajirin da ya ke sananne ga babban firist ya fita, yayi magana da macen da ta ke tsaron kofar, sa'an nan ya shigo da Bitrus.
17 The servant girl who was guarding the doorway said to Peter, “Surely you are not another disciple of that man [they have arrested], are you?” He said, “I am not.”
Sai yarinyar mai tsaron kofar ta ce wa Bitrus, ''kai ma ba kana cikin almajiran mutumin nan ba?'' Yace ''bani ba.''
18 It was cold, so the high priest’s slaves and Temple guards made a charcoal fire and were standing around it to keep warm. Peter was also standing near it, warming himself.
To, barorin da dogaran Haikali suna tsaye a wurin, sun kuwa hura wutar gawayi, suna jin dumi, gama ana sanyi. Bitrus ma yana tsaye tare da su yana jin dumin.
19 [While Peter was doing that], the high priest asked Jesus about his disciples and about what he was teaching people.
babban firist ya tambayi Yesu game da almajiransa da koyarwarsa kuma.
20 Jesus replied, “I have always spoken where many people [MTY, HYP] could hear me. I have taught them in (the synagogues/their meeting places) and in the Temple courtyard, in places where many [HYP] Jews come together. I have spoken nothing secretly.
Yesu ya amsa masa, Ai, na yi wa duniya magana a bayyane. Na kuma sha koyarwa a majami'u da Haikali in da Yahudawa duka sukan taru. Ban fadi komai a boye ba.
21 [So] (why are you asking me questions [like this illegally]?/you should not be asking me questions [like this illegally]!) [RHQ] Ask the people who heard what I taught! They certainly know what I said!”
Don me kake tambaya ta? Ka tambayi wadanda suka saurare ni a kan abinda na fada, ai, sun san abinda na fada.
22 After Jesus said that, one of the Temple guards standing near him slapped him on his face. He said, “(That is not the way you should answer the high priest!/Is that the way you should answer the high priest?) [RHQ]”
Sa'adda Yesu ya fadi wannan, wani daga cikin 'yan majalisar da ke tsaye a wurin ya nushi Yesu, yace, ''Kana amsa wa babban firist haka.''
23 Jesus replied to him, “If I said something that was contrary [to your laws], you could tell [me that what I said that] was wrong. But because I said only what was right, (you should not be striking me!/why are you striking me?) [RHQ]”
Yesu ya amsa masa yace, ''Idan na fadi mugun abu to, ka bada shaida kan hakan. In kuwa dai dai na fada, to, dan me za ka nushe ni?''
24 Then after Jesus’ hands were tied {after they tied Jesus hands} [again], Annas sent him to Caiaphas, the high priest.
Sai Hanana ya aika daYesu a daure wurin Kayafa, babban firist.
25 As Simon Peter was standing warming himself [at the fire], someone else said to him, “You are not one of that man’s disciples, are you?” He denied [that he was], and said, “I am not.”
To Saminu Bitrus yana tsaye yana jin dumin. Mutanen kuwa suka ce masa, ''Anya kai ma ba cikin almajiransa ka ke ba?'' Sai yayi musu yace, ''A'a, ba na ciki.''
26 [Later] one of the high priest’s servants, a man who was a relative of the man whose ear Peter had cut off [before], said to him, “I saw you with that man in the grove [of olive trees], did I not?”
Sai wani daga cikin bayin babban firist, wato dan'uwan wanda Bitrus ya fillewa kunne, yace, ''Ashe, ban gan ka tare da shi a lambun ba?
27 Peter again denied it. Immediately a rooster crowed, [as Jesus had said would happen].
Bitrus ya sake yin musu, nan da nan kuwa zakara yayi cara.
28 Then the [Jewish leaders] [SYN] led Jesus from the [home of] Caiaphas to the headquarters [of Pilate, the Roman governor]. It was before dawn. [Pilate was a non-Jew], [and they thought that if they entered his headquarters], they would become unacceptable to God {God would reject them}, [and as a result] they would not be able to eat [the food during] the Passover [celebration]. [Because of that, they did not want to enter Pilate’s headquarters].
Daga wurin Kayafa kuma suka kai Yesu fadar Gwamna. Da asuba ne kuwa, su kansu ba su shiga fadar Gwamnan ba, wai don kada su kazantu su kasa cin jibin Ketarewa.
29 So Pilate came out to [talk to] them. He said, “What law do you say that this man has disobeyed?”
Sai bilatus fa ya fita zuwa wurinsu, yace, 'Wane zargi ku ke kawowa akan mutumin nan?'
30 [They knew that Jesus had not disobeyed any Roman law, so they did not want to answer him. Instead], they said, “If this man were not a criminal, we would not have brought him to you!”
''Sai suka amsa suka ce, ''idan da mutumin nan bai yi mugun abu ba, me zai sa mu yi kararsa a wurin ka''
31 Then Pilate said to them, “Take him yourselves, and judge him according to your own laws!” Then the Jewish [leaders] [SYN] said, “[No! We want him executed, but we want you Romans to execute him, because] we Jews have no right to execute anyone!”
bilatus yace masu, ''Ku tafi da shi da kan ku mana, ku hukunta shi bisa ga shari'arku!'' Sai Yahudawa su kace masa, ''Ai, ba mu da ikon zartar da hukuncin kisa akan kowa.''
32 [The Romans executed people by nailing them to a cross]. [So], as a result of what [the Jewish leaders said], it was fulfilled {[the Romans] would fulfill} what Jesus had said previously about the way he was going to die.
Sun fadi Wannan ne don a cika maganar da Yesu yayi, wadda ta kwatanta irin mutuwar da zai yi.
33 Pilate then went back inside his headquarters. He summoned Jesus. [Because the Jewish leaders had said that Jesus claimed to be a king], Pilate said to Jesus [scornfully], “Are you the king of the Jews?”
Sai bilatus ya sake shiga cikin fadar Gwamnan, ya kira Yesu ya ce masa, ''kai sarkin Yahudawa ne?''
34 Jesus replied, “Are you asking that because you yourself [want to know if I claim to be a king], or because (someone else/Caiaphas) said [that I claim to be their king]?”
Yesu ya amsa, '' wannan fadarka ce, ko kuwa wadansu ne suka ce da ni haka a wurinka?''
35 Pilate replied, “I am not a Jew, [so] ([I cannot understand these matters!/how can I understand these matters]?) [RHQ] It was your fellow Jews and your chief priests who brought you to me! What have you done [to make them want to execute you]?”
Bilatus ya amsa “Ni ba Bayahude bane, ko kuwa?'' Ai, jama'arka ne da manyan firistoci suka bashe ka gareni. ''Me ka yi?''
36 Jesus replied, “It is not people in [MTY] this world who are [making me] king. If it was people in this world who were making me a king, my disciples would have fought in order that the Jewish [leaders] [SYN] would be prevented {to prevent the Jewish [leaders] [SYN]} from seizing me. But it is not [someone here in] this world who is making me a king.”
Yesu ya amsa, ''Mulkina ba na duniya nan ba ne. Da mulkina na duniyan nan ne da barorina za su yi yaki kada a bashe ni ga Yahudawa. To, mulkina ba daga nan ya ke ba.''
37 Then Pilate said to him, “So [are you saying that] you are a king?” Jesus replied, “[Yes], what you have said about my being a king [is correct]. I was born to become a king, and I came into this world to tell people the truth [about God]. Everyone who [believes] the truth pays attention to what I say.”
Sai Bilatus yace masa, ''Wato ashe, sarki ne kai?'' Yesu ya amsa, ''Yadda ka fada, ni sarki ne. Domin wannan dalili aka haife ni, domin kuma wannan dalili na zo cikin duniya, don in bada shaida game da gaskiya. Kowane mai kaunar gaskiya kuma yakan saurari muryata.''
38 Pilate said to him, “[How can anyone know] what the truth is?” After he said that, he went outside and talked to the Jewish [leaders] [SYN] again. He said to them, “I do not find that he has done anything at all for which I should punish him.
Bilatus yace masa, ''Menene gaskiya?'' Bayan da ya fadi haka, ya sake fitowa wurin Yahudawa, yace masu, ''Ni kam, ban sami mutumin nan da wani laifi ba.
39 But you [Jews] customarily, [every year] during the Passover [celebration], ask me to release for you [someone who is in prison]. So would you like for me to release for you the [man who you] Jews [say is your] king?”
Amma dai kuna da wata al'ada, in Idin Ketarewa ya yi, na kan sakar maku mutum daya. To, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?''
40 They shouted again, “No, do not [release] this man! Instead, [release] Barrabas!” But Barrabas was [in prison because he was] a revolutionist!
Sai suka sake daukar kururuwa suna cewa, ''A; a, ba wannan mutum ba, sai dai Barabbas.'' Barabbas din nan kuwa dan fashi ne.