< John 17 >

1 After Jesus said those things, he looked [up] toward heaven. Then he prayed, “[My] Father, it is now the time [MTY] [for me to suffer and die]. Honor me [as I do that], in order that I may honor you.
Bayan da Yesu ya faɗi wannan, sai ya dubi sama ya yi addu’a ya ce, “Uba, lokaci ya yi. Ka ɗaukaka Ɗanka, don Ɗanka yă ɗaukaka ka.
2 You gave me authority over all people, in order that I might enable all those whom you chose [to come] to me to live eternally. (aiōnios g166)
Gama ka ba shi iko bisa dukan mutane domin yă ba da rai madawwami ga duk waɗanda ka ba shi. (aiōnios g166)
3 [The way for people] to live eternally is for them to know that you are the only true God, and to know that [I], Jesus, am the Messiah, the one you have sent. (aiōnios g166)
Rai madawwami kuwa shi ne, su san ka, Allah makaɗaici mai gaskiya, da kuma Yesu Kiristi, wanda ka aiko. (aiōnios g166)
4 I have honored you here on this earth by completing all the work that you gave me to do.
Na ɗaukaka ka a duniya ta wurin gama aikin da ka ba ni.
5 [My] Father, now honor me when I am with you [again], by causing me to have the greatness I had when I was with you before the world began.”
Yanzu ya Uba, ka ɗaukaka ni a gabanka da ɗaukakar da dā nake da ita tun kafin a kafa duniya.
6 “I have revealed [what] you [are like] to the people whom you brought to me from among those who do not belong to you [MTY]. Those [who came to me] belonged to you, and you brought them to me. Now they have obeyed your message.
“Na bayyana ka ga waɗanda ka ba ni a duniya. Su naka ne; kai ka ba ni su sun kuma yi biyayya da maganarka.
7 Now they know that everything you have given me, [your message and your work], comes from you.
Yanzu sun san cewa duk abin da ka ba ni daga gare ka ya fito.
8 I gave them the message that you gave me, and they have accepted it. They now know for certain that I came from you. They now believe that you sent me.
Na ba su kalmomin da ka ba ni sun kuwa karɓa. Sun san tabbatacce daga wurinka na fito. Sun kuma gaskata kai ka aiko ni.
9 I am praying for them. I am not praying for those [who do not belong to you] [MTY]. Instead, [I am praying] for those whom you have brought to me, because they belong to you.
Ina addu’a dominsu. Ba domin duniya nake addu’a ba, amma domin waɗanda ka ba ni, gama su naka ne.
10 All [the disciples] that I have belong to you, and all those who belong to you also belong to me. They have shown how great I am.
Duk abin da nake da shi naka ne, kuma duk abin da kake da shi nawa ne. Na kuwa sami ɗaukaka ta wurinsu.
11 I will not be [staying] in the world any longer. I will be coming back to you. They, however, will be [here] in the world [among those who are opposed to you]. [My] Holy Father, protect them from spiritual harm by your power [MTY], the power that you gave me, in order that they may be united as we are united.
Ba sauran zamana a duniya, amma waɗannan a duniya suke, ni kuwa ina zuwa wurinka. Ya Uba Mai Tsarki, ka kiyaye su ta wurin ikon sunanka, sunan da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya.
12 While I have been with them, I have [completely] protected them by the power [MTY] that you gave me. As a result, only one of them will be eternally separated from you. He is the one who was doomed to be eternally separated from you. [That has happened] to fulfill [what a prophet wrote] in the Scriptures [would happen].
Yayinda nake tare da su, na kāre su na kuma kiyaye su ta wurin sunan nan da ka ba ni. Ba ko ɗayan da ya ɓace, sai dai wannan da aka ƙaddara zuwa ga hallaka don Nassi yă cika.
13 [Father], now I am about to return to you. I have said these things while I am still [here] in the world in order that my [disciples] may fully experience being joyful, as I have been joyful.
“Yanzu ina zuwa wurinka, sai dai na faɗi waɗannan abubuwa ne tun ina a duniya domin farin ciki yă zama cikakke a cikinsu.
14 I have given them your message. As a result, those who are opposed to you [MTY] have hated them, because [my disciples] do not belong to those who oppose you [MTY], just like I do not belong to those who oppose you [MTY].
Na gaya musu maganarka duniya kuwa ta ƙi su, don su ba na duniya ba ne yadda ni ma ba na duniya ba ne.
15 I am asking you, not that you take them out of this world, but instead that you protect them from [Satan], the evil one.
Ba addu’ata ba ce ka ɗauke su daga duniya ba, sai dai ka kāre su daga mugun nan.
16 They do not belong to those who are opposed to you [MTY], just like I also do not belong to them.
Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ma ba na duniya ba ne.
17 Set [my disciples] apart so that they may (completely belong to/serve) you, by [enabling them to live in accordance with] what is true. Your message is true.
Ka tsarkake su ta wurin gaskiya; maganarka ce gaskiya.
18 Just like you sent me here into this world, now I surely will be sending them [to other places] in [MTY] the world.
Kamar yadda ka aiko ni cikin duniya, haka ni ma na aike su cikin duniya.
19 I dedicate myself to completely belong to you, in order that they also may truly be dedicated {dedicate themselves} completely to you.”
Saboda su ne na tsarkake kaina, domin su ma a tsarkake su da gaske.
20 “I am praying not only for these [eleven disciples]. I am praying also for those who [will] believe in me as a result of [hearing] their message.
“Addu’ata ba saboda masu bina kaɗai ba ne. Ina addu’a kuma saboda waɗanda za su gaskata da ni ta wurin maganarsu.
21 [My] Father, [I want] all of them to be united, just like I am united with you because of my relationship with you, and as you are united with me because of your relationship with me. I also want them to be united with us. [I want that to happen] so that those who do not know you [MTY] may know that you sent me.
Ina so dukansu su zama ɗaya, ya Uba, kamar yadda kake a cikina, ni kuwa a cikinka. Haka su ma bari su zauna cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa kai ka aiko ni.
22 I have honored my disciples just like you honored me, in order that they may be united, as we are united.
Na ba su ɗaukakar da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya.
23 I want them to be united just like they are united with me and as you are united with me. May they be completely united, in order that those who do not belong to you [MTY] may know that you sent me and that you have loved them just like you have loved me.
Ni a cikinsu kai kuma a cikina. Bari su kasance da cikakken haɗinkai, domin duniya ta san cewa kai ka aiko ni. Ka kuwa ƙaunace su yadda ka ƙaunace ni.
24 [My] Father, I want [the disciples] you have brought to me to [some day] be with me [in heaven], where I will be. I want them to see my greatness. I want them to see the greatness you gave me because you loved me. You gave me that greatness before you created the world.
“Uba, ina so waɗanda ka ba ni su kasance tare da ni a inda nake, su kuma ga ɗaukakata, ɗaukakar da ka ba ni domin kana ƙaunata kafin halittar duniya.
25 [My] righteous Father, although the people who do not belong to you [MTY] do not know what you [are like], I know what you [are like], and my disciples know that you sent me.
“Ya Uba Mai Adalci, ko da yake duniya ba tă san ka ba, ni na san ka, sun kuma san kai ka aiko ni.
26 I have revealed to them [what] you [are like], and I will continue to reveal to them [what] you [are like]. I will do that in order that they may love [others] just like you love me, and in order that I may be in them [by my Spirit].”
Na bayyana ka a gare su, zan kuma ci gaba da bayyana ka domin ƙaunar da ka yi mini ta kasance a cikinsu ni ma in kasance a cikinsu.”

< John 17 >