< Job 7 >
1 “People need to work hard on this earth, like soldiers do; all during the time that we are alive, we work hard [RHQ], like laborers/servants do.
“Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
2 We are like [SIM] slaves who keep wanting to be in the cool shade, and we are like [SIM] workers who are waiting to be paid.
Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
3 God has given me many months [in which I think that it is] useless [to remain alive]; he has allotted/given to me many nights during which I feel miserable.
Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
4 When I lie down [at night] I say, ‘How long will it be until morning?’ But nights are long, and I (toss/turn over and over) [on my bed] until dawn.
Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
5 My body is covered with maggots and scabs; pus oozes out of my open sores.
Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
6 My days pass as quickly as a weaver’s (shuttle/stick that takes the thread back and forth), and they end without my confidently expecting [that things will be better the next day].
“Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
7 God, do not forget that my life is [as short as] a breath [MET]; I [think that] I [SYN] will never again be happy.
Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
8 God, you [SYN] see me now, but [some day] you will not see me any more. You will search for me, but I will be gone [because I will be dead].
Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
9 Like [SIM] clouds (disperse/break up) and then disappear, people [die and] descend to the place where dead people are, and they do not return; (Sheol )
Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol )
10 they never return to their houses, and people among whom they lived do not remember them any more.
Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
11 So, I will not be silent; while I am suffering I will speak; I will complain [to God about what has happened to me] because I [SYN] am very angry.
“Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
12 [God, ] why do you watch closely what I am doing? [Do you think that] I am a [dangerous] sea monster?
Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
13 When [I lie down at night, ] I think, ‘I will be comforted here on my bed; my pain will be less while I am sleeping.’
Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
14 But then you give me dreams that cause me to be afraid; you give me visions that terrify me,
duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
15 with the result that I would prefer to be strangled to death than to continue to [be alive] being only a bunch of bones.
Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
16 I detest continuing to be alive; I do not want to live for many years [HYP]. Allow me to be alone, [because I will be alive] for only a very short remaining time [HYP].
Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
17 “We human beings are not [very important]; so, why do you pay a lot of attention to us [DOU]?
“Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
18 You look at us every morning [to see what we are doing], and examine us every moment [to see if we are doing what is right].
har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
19 (When will you stop looking at me and leave me alone [for a little time], long enough to swallow my spit?/Please stop looking at me and leave me alone [for a little time], long enough to swallow my spit.) [RHQ]
Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
20 [Why do] you watch me constantly? If I sin, that certainly does not harm you! Why have you set me up like a target to shoot at? Do you consider me to be a heavy load that you are forced to carry?
In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
21 [If I have sinned, ] are you not able to forgive me for my sins— the things that I have done that are wrong? Soon I will lie in my grave; you will search for me, but [you will not find me because] I will be [dead and] gone.”
Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”