< Job 33 >
1 “But now, Job, listen carefully to all that I am going to say [DOU].
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 I am ready to tell you [MTY, DOU] [what I think].
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 I know that I am speaking honestly and that I am speaking [MTY] sincerely.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 Almighty God has created me [as well as you], and his breath has caused me to live.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 So, answer [what] I [say] if you can; think carefully [about how you will reply to me].
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 “God considers that you, and I are both [equal]; he formed both of us from clay.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 So you do not need to be afraid of me; I will not crush/oppress you [by what I say] [MTY].
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 I have heard you [DOU] speaking, and this is what you have said:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 ‘I am innocent; I have not committed any sins; I am pure; I have not done things that are wrong.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 But God finds reasons to accuse me, and he considers that I am his enemy.
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 [It is as though] he has put my feet (in stocks/between wooden blocks to prevent me from walking away), and he watches everything that I do.’ [MTY]
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 But what you have said is wrong, and I will tell you [what you have said that is wrong]. God is much greater than any human.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 So, (why are you arguing against God, saying ‘He never answers my questions’?/you should not be arguing against God, saying ‘He never answers my questions.’) [RHQ]
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 God does speak [to us] in various ways, but we do not pay any attention to what he says.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 [Sometimes he speaks to us] at night in dreams and visions, when we are on our beds, asleep [DOU].
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 He reveals things [MTY] to us and terrifies us by the things he warns us about.
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 He tell us those things in order that we stop doing [evil] things and to prevent us from becoming proud.
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 He does not want us to be destroyed [MTY]; he wants to prevent us from dying [MTY] [while we are still young].
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 God also [sometimes] corrects us by forcing us to lie on our beds suffering much pain and with fever/aching in our bones.
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 The result is that we do not desire any food, not even very special food.
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 Our bodies become very thin, with the result that we look like skeletons [HYP], and our bones stick out.
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 [We know that] we will soon die and go to the place where dead people are.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 “But sometimes an angel [may come to one of us], one of the thousands of angels who come to intervene between us and God, to tell us what are the right things for us [to do].
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 The angel is kind to us and says to God, ‘Release that person, so that he does not descend to the place where dead people are! Do that because I have found the money to pay so that he can be released!
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 Allow his body to be strong again; allow him to be strong like he was when he was a youth!’
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 When that happens, that person will pray to God, and God will accept/answer him; he will (enter God’s presence/worship God) joyfully, and then he will tell others how God saved him [from dying].
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 He will sing as he tells everyone, ‘I sinned, and I did things that were not right, but God did not punish me in the way that I deserved.
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 He has saved me from dying and going to the place where dead people are, and I will continue to enjoy being alive.’
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 God does all these things for us many times;
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 he keeps us [SYN] from [dying and] going to the place where the dead are, in order that we can continue to enjoy being alive [IDM].
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 So Job, listen to me; do not say anything more; just allow me to speak.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 [After I speak], if you have something more that you want to say to me, say it, because I would like to find a way to declare that you (are innocent/have not done what is wrong).
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 But if you have nothing more that you want to say, then just listen to me, and I will teach you how to become wise.”
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”