< Job 32 >

1 Then those three men stopped answering Job, because [they could not convince Job that he was wrong in claiming that] he had not done anything that was wrong.
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
2 Then Elihu, the son of Barachel, a descendant of Buz, from the clan of Ram, became very angry at Job. He was angry because Job continued to claim that he was righteous/innocent, and that God was wrong [to punish him].
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
3 He was also angry with Job’s three friends, because they had declared that Job must have done many things that were wrong, but they were unable to convince Job [that what they said was true]. As a result, [it seemed to Elihu that] God did what was wrong by punishing Job.
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
4 Elihu was younger than the others, so he waited [until they had finished speaking] before he replied to Job.
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
5 But when Elihu realized that the three men had no more to say [MTY] to Job, he became angry.
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
6 And this is what he said: “I am young, and you all are much older than I am. So, I was timid, and I was afraid to tell you what I was thinking.
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
7 I thought, ‘Let those [PRS] who are much older speak, because older people [should be able to] say things that are wise.’
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
8 But the Spirit of Almighty [God] is within people, and it is he who enables them to be wise.
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
9 It is not people becoming old that enables them to be wise; not [all] old people understand what is right.
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
10 “So, I say, ‘Listen to me, and allow me to say what I think.’
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
11 I waited for you all to speak; I wanted to hear the wise things that you would say. I waited while you thought carefully about what [would be the right things] to say.
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
12 I paid attention carefully, but surprisingly, none of you were able to prove that what Job said was wrong.
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
13 So, do not say [to yourselves], ‘We have discovered what is wise!’ It is God who must (refute Job/show that what Job said was wrong), because you three have not been able to do that.
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
14 Job was replying to you, [not to me], but I will not reply to him by saying what you three said.
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
15 “You three are dismayed [because you have not been able to convince him that he was wrong], so you are not saying any more to him [DOU].
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16 But because you do not speak, I certainly will not wait any longer [RHQ]; you merely stand there and do not reply any more.
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17 So [now] I also will reply [to Job] and say what I think.
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18 I have plenty to say, and my spirit compels me to say it.
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19 My inner being is like [SIM] a (wineskin/bag that has (new/fermenting) wine in it), and it will soon burst.
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20 I must speak [MTY], in order that I do not have to keep holding what I want to say; I must say something [MTY] to reply [to you all].
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21 I will speak [fairly], not favoring any of you, and I will not try to flatter anyone.
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22 I [really] do not know how to flatter people; and if I did that, God would soon get rid of me.”
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.

< Job 32 >