< Job 30 >

1 “But now men who are younger than I am make fun of me— men whose fathers I greatly despised, with the result that I would not even have allowed them to help my dogs guard my sheep.
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 They were men who were old and (weak/worn out); so (what could I gain from them working for me?/I would have gained nothing from them working for me.) [RHQ]
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 They were very poor and hungry, with the result that they chewed on roots [at night] in dry and desolate places.
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 They pulled up plants in the desert [and ate them] and warmed themselves by [burning] the roots of broom trees.
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 Everyone shouted at them as though they were thieves and expelled them [from their areas].
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 They were forced to live in caves in the hills, in holes in the ground, and in the sides of cliffs.
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 In the bushes they howled [like animals because they were hungry], and they huddled together under thornbushes.
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 They were people without good sense, whose names no one knows; they have been expelled from the land [where they were born].
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 “And now their [children] sing songs to make fun of me. They tell jokes about me.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 They are disgusted with me, and they [usually] stay away from me, [but when they see me, ] they are happy to spit in my face.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 Because [it is as though] [MET] God has cut my bowstring, [he has caused me to be unable to defend myself, ] and he has humbled me, and my enemies have done to me whatever they wanted.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 (Gangs/Groups of violent youths) attack me and force me to run away; they prepare to destroy me.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 They prevent me from escaping, and they [do] not [need] anyone to help them (OR, there is no one to help me).
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 [It is as though I am a city wall and] [SIM] they have broken through the wall, and they have come crashing down on me.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 I am very terrified; My dignity/honor has been taken away as though [SIM] [it has been] blown away by the wind, and my prosperity has disappeared like [SIM] clouds disappear.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 “And now I [SYN] am about to die [IDM]; I suffer every day.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 My bones ache during the night, and the pain that torments me never stops.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 [It is as though God] seizes my clothes and chokes me with the collar of my coat.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 He has thrown me into the mud; I am [not worth anything more than] dust and ashes.
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 “I cry out to God, but he does not answer/help me; I stand up [and pray], but he does not pay any attention.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 He acts very cruelly toward me; with all of his power [MTY] he causes me to suffer.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 He [allows] the wind to lift me up and blow me away, and he tosses me up and down in a violent storm.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 I know that he will cause me to die, which is what happens to everyone [MTY] who is alive.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 “When people experience disasters, and they sit on a pile of ruins and cry out for help, others surely [RHQ] reach out their hand to help them.
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 [That is what I did previously]. I wept for people who were experiencing troubles, and I felt sorry for poor/needy people.
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 But when I expected good things [to happen to me], evil things happened; when I waited for light/happiness, all I experienced was darkness/unhappiness [MET].
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 I am very distressed [IDM], all the time; I suffer every day.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 I go about very discouraged; I stand up and plead for people to help me.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 My wailing sounds as sad as [MET] the cries of jackals/foxes and ostriches.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 My skin has become dark/black and is peeling off, and I have a fever [which causes my body to feel like it is] burning.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 Previously, I played joyful music on my harp and with my flute, but now I play only the sad music of those who mourn.”
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.

< Job 30 >