< Job 3 >
1 Finally, Job spoke, and he cursed the day that he was born.
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
3 “I wish that the day when I was born could be eradicated, and also the night when I was conceived.
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4 I wish that the day when I was born would have been covered in darkness. I wish that God who is in heaven [MTY] would have forgotten about that day, and that the sun would not have shone on it.
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5 I wish that thick/intense darkness would have filled that day, and that a black cloud would have come over it and blotted out all light and caused people to be terrified.
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6 I wish that the night when I was conceived would be erased from the calendar, with the result that it would never again appear as one night in any month, and that it would not be included in any calendar.
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7 I wish that no child would again be conceived on that night of the month [MET], and that no one would again be happy on that night.
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8 I want those people who (curse/put evil spells on) days—those who know how to arouse/awaken the great sea monster—to curse that day.
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9 I wish that the stars that shone early in the morning on that day [after I was conceived] will not shine again. I want those stars to have wished in vain for light to shine; and that they would not have shone on that day.
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10 [That was an evil day] because my mother was able to conceive; instead, I was born, and I have now experienced all these terrible things.
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11 “I wish that I had died [RHQ] when I was born— at the time I emerged from my mother’s womb.
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12 I wish that my mother had not [RHQ] allowed me to live. I wish that she had not nursed me.
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13 If I had died at the time when I was born, I would be asleep, resting peacefully [in the place where the dead people are].
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14 I would be resting with kings whose [beautiful palaces] that they built are now in ruins (OR, who rebuilt [palaces] that had previously been destroyed), and I would be resting with their officials [who have also died].
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15 I would be resting with princes who were wealthy, whose palaces were filled with gold and silver.
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16 I wish that I had been buried like a child who died in its mother’s womb and never lived to see the light.
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
17 After wicked people die, they do not cause any more troubles; those who are very tired now will rest.
A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
18 Those who were in prison rest peacefully [after they die]; they no longer have slave-drivers who curse them.
Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
19 Rich people and poor people are alike after they die, and those who were slaves are no longer controlled by their masters.
Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
20 (“Why does God allow those who are suffering greatly [like me] to continue to remain alive?/I do not understand why God allows those who are suffering greatly [like me] to continue to remain alive.) [RHQ] Why does he allow those who are very miserable/distressed to keep living [RHQ]?
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21 They long/want to die, but they do not die. They desire to die more than people desire to find a hidden treasure.
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22 When they finally die and are buried, they are very happy.
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23 Those who do not know where they are [eventually] going when they die [RHQ], people whom God has forced [MET] to continue to live in misery, (it is not right that they continue to live./why do they continue to live?) [RHQ]
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24 I continually cry very much; as a result, I cannot eat; and I can never stop groaning.
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25 Things that I always worried might happen to me, have happened to me; things that I always dreaded have happened to me.
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26 Now I have no peace [in my inner being], I have no peace; I cannot rest; instead, I have only troubles.”
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”