< Job 29 >

1 Job spoke again,
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 “I wish/desire that I could be like I was previously, during the years when God took care of me.
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3 During those years, [it was as though] God’s lamp [MET] shone on me and gave me light while I walked in the darkness.
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 At that time I was young and strong, and because God was my friend, [he protected] [PRS] my tent.
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5 Almighty [God] was with me during those years when all my children were around me.
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
6 [My herds] provided me with plenty of milk, and streams of oil flowed from the rock where my olives were pressed.
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7 “Whenever I went to [the place where the elders gathered at] the city gate, I sat down with them,
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8 and when the young men saw me, they stepped aside [respectfully], and the old men [also] stood [respectfully].
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9 The leaders of the people stopped talking [DOU],
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10 and even the most important men became quiet and ceased talking [MTY] [in order to hear me speak to them].
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 When they [SYN] all heard [what I told them], they said good things about me. When they [SYN] saw me (OR, what I had done), they commended me,
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12 because I had helped the poor people when they cried out for help and I aided/helped orphans who had no one else to help them.
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13 Those who were suffering and about to die praised [PRS] me, and I caused widows [SYN] to sing joyfully, [because of my helping them].
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14 I always acted justly; my continually doing that was like [MET] a robe that I wore and a turban [that was wrapped around my head].
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15 [It was as though] [MET] I was eyes for blind people and feet for people who were lame.
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 I was [like] [MET] a father to poor people, and in courts I defended those who were strangers.
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 My causing wicked people [to be unable to continue oppressing others was like] [MET] breaking the fangs [of fierce wild animals] and forcing them to drop from their teeth/mouths the animals that they had caught/seized.
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 “At that time I thought, ‘Surely I will live securely, until I am very old [SIM], and I will die at home [with my family].’
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
19 I was [like a tree] [MET] whose roots reach down into the water and whose branches become wet with dew each night.
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
20 People always honored me, and I was always [strong like] [MET] a new bow.
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
21 “When I spoke, people waited to hear [what I would say] and remained silent until I advised them [what they should do].
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 After I finished speaking, they did not say any more; [it was as though] [MET] my words fell on their ears [like refreshing drops of rain].
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23 They waited for me [to speak] like they wait for rain; they [appreciated what I said] like [MET] [farmers appreciate] the final rain in the spring [before the dry season].
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 When they were discouraged, I smiled at them [to encourage them]; they became encouraged when they saw that I approved of them.
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 I was their leader, and I decided what things [would be good for them to do]; I was among them like [SIM] a king who is among his troops; I was like someone who comforts [others] who are mourning.”
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.

< Job 29 >