< Job 19 >

1 Then Job replied:
Sai Ayuba ya amsa,
2 “How long will you [three] torment me and crush my spirit by saying to me [that I am wicked]?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 You have already insulted me many [HYP] times; (are you not ashamed for saying these things to me?/you should be ashamed for saying these things to me.) [RHQ]
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 Even if it were true that I have done things that are wrong, I have not injured you!
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 If you truly think that you are better than I am, and you think that my being miserable now proves that I (am guilty/have committed many sins),
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 you need to realize that it is God who has caused me to suffer. [It is as though] he has trapped me with his net.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 “I cry out, ‘Help me!’, but no one answers me. I call out loudly, but there is no one, [not even God, ] who acts fairly toward me.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 [It is as though] [MET] God has blocked my way, with the result that I cannot go where I want to; [it is as though] he has forced me to try to find my way in the darkness.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 He has (taken away my good reputation/caused people not to honor me any more); [it is as though] he removed [MET] a crown from my head.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 He batters me from every side, and I will soon die. He has caused me to no longer confidently expect [him to do good things for me].
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 He attacks me because he is extremely angry with me [MET], and he considers that I am his enemy.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 [It is as though] he sends his army to attack me; they surround my tent, preparing to attack me.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 “God has caused my brothers to abandon me, and all those who know me act like strangers to me.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 All my relatives and good friends have left me.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 The people who were guests in my house have forgotten me, and my female servants consider that I am a stranger or that I am a foreigner.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 When I summon my servants, they do not answer; I plead with them to come [to help me, but they do not come].
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 My wife does not want to come close to me because my breath [smells very bad], and even my brothers detest me.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Even young children despise me; when I stand up [to talk to them], they laugh at me.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 My dearest friends detest me, and those whom I love [very much] have turned against me.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 My body is [only] skin and bones; I am barely alive [IDM].
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 [“I plead with] you, my [three] friends, pity me, because God has (struck [EUP] me with his hand/caused me to suffer greatly).
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Why do you cause me to suffer like God does? Why do you continue to slander [MET] me?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 “I wish/desire that someone would take these words of mine and write them permanently in a book [in order that people can read them].
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 Or else, I wish that he would carve them on a rock with (a chisel/an iron tool) in order that they would last forever.
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 But I know that the one who vindicates/defends me in court is alive, and that some day he will stand [here] on the earth [and make the final decision about whether I deserve to be punished].
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 And even after diseases have eaten away my skin, while I still have my body, I will see God.
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 I will see him myself; I will see him with my own eyes! I am overwhelmed [as I think about that]!
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 “If you three men say, ‘What more can we do to cause Job to suffer?’ and if you say, ‘He has caused his own [troubles],’
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 you should be afraid that God will punish [MTY] you; he punishes those [like you] with whom he is angry; and when that happens, you will know that there is [someone who] judges [people].”
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< Job 19 >