< Job 13 >

1 “Hey, I [SYN] have seen everything [that you have seen], and I have heard and understood all [that you have said].
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 What you know, I also know; I do (not know less than/know as much as) you.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 But I would like to speak to Almighty God, [not to you]; I would like to argue with him [and prove that I (am innocent/have not done things that are wrong]).
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 As for you, you do not allow people to know the truth about me, like someone covers [up a bad surface of a wall] with whitewash [MET]. You are all like doctors [MET] [that give people] useless [medicines].
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 I wish/desire that you would be silent; that would be the wisest thing that you [could do].
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Listen to what I will say to you now; listen while I am saying [what is true about myself].
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Are you telling lies about me to prove God [is just in causing me to suffer]? Are you saying what is deceitful in order to benefit him?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Are you trying to defend him? Are you trying to prove [as you would] in a court that he is innocent?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 If he looks closely, will he find that everything that you have done is good? Or can you deceive him, like you deceive other people?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 If you secretly say/do things to cause God to act favorably toward you, he will surely rebuke you.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 He will certainly [RHQ] cause you to be terrified by his power/greatness; you will become extremely afraid.
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 The things that you say [that you think are] wise are [as useless as] [MET] as ashes; what you say to defend your opinions is no better than [MET] clay [that quickly crumbles].
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 “So, be quiet and allow me to speak, and then it will not matter what happens to me.
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 I am ready to endure anything; I am [even] willing to risk being executed [IDM, DOU] [for what I will say].
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 If God kills me, then I will not have anyone else whom I can confidently expect to help me, but I am going to defend my behavior in his presence [anyway].
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 No wicked/godless person would dare to stand in the presence of God, [but because I say that I have not done things that are wrong], perhaps, if I can prove that to God, he will save me.”
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 “God, listen very carefully to what I say [DOU].
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 I am ready to prove that I am innocent, and I know that you also will declare that I am not guilty.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 I certainly do not think [RHQ] that [you or anyone else] will say that what I say is not true; if anyone did that, I would (be silent/stop talking) and die.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 “I am requesting you to do two things for me; if you do them, I will (not hide from you/come and stand in front of you) [LIT].
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 [The first thing that I request is that you] stop punishing [IDM] me; and [the second thing that I request is that you] stop causing me to be very terrified.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 You speak [first], and then I will reply; or allow me to speak first, and [then] you reply.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 What have I done that is wrong? What sins have I committed? Show me how I have disobeyed you.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Why (do you refuse to be friendly with/have you abandoned) me [IDM]? Why do you (act toward me as though I am/consider me to be) your enemy?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 I am [as insignificant as] [MET] a leaf that is blown by the wind; why are you trying to cause me to be afraid [RHQ]? Why are you pursuing me? Am I [useless, nothing more than a bit of] dry chaff [RHQ]?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 [It seems that] you are writing things to accuse me [of doing things that are wrong], even recalling bad things that I did when I was young.
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 [It is as though] you have fastened my feet with chains [to prevent me from walking], and you watch me wherever I walk; [It is as though] you even look closely at my footprints [to see where I have gone].
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 [As a result], my body is decaying like [SIM] rotten wood, like a piece of cloth that is eaten by [larvae of] moths.”
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.

< Job 13 >