< Jeremiah 46 >

1 These are messages that Yahweh gave to the prophet Jeremiah about [other] nations.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
2 After Jehoiakim, son of King Josiah, had been ruling Judah for almost four years, this message about Egypt was given [by Yahweh]. It was when the army of King Neco of Egypt was defeated by the army of King Nebuchadnezzar of Babylon along the Euphrates River. [This is what Yahweh said: “The officers of the army of Egypt are saying to their troops],
Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
3 ‘Prepare your shields and march out to fight the battle!
“Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
4 Put harnesses on your horses, and get on their backs. (Get into your positions/Line up) [for the battle]; put on your helmets. Sharpen your spears, and put on your armor!’
Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
5 But what [RHQ] do I see? I see that the soldiers of Egypt will be terrified and will be fleeing. [Even] the bravest of their soldiers will be running away, without [even] looking backward! [I, ] Yahweh, say that [their soldiers] will be terrified on all sides!
Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
6 [Even] the fastest [runners] will try to run away, but [even the greatest of] their warriors will not escape. In the north, by the Euphrates [River], they will stumble and fall.
“Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
7 What group is this that will be covering the land like the water of the Nile [River] covers the land when it floods?
“Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
8 [It is the army of] Egypt that will be covering the land like a surging/huge flood, and they will boast that they will cover the earth and will destroy cities and the people [who live in them].
Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
9 You [riders of] horses, charge/rush [into the battle]! You [drivers of] chariots, drive furiously! [All] you warriors from Ethiopia and Libya who carry your shields, you warriors from Lydia who shoot arrows, you come!
Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
10 But, [you need to know that] this is the day when [I], Yahweh, the Commander of the armies of angels, will get revenge on my enemies. With my sword [PRS] I will kill [my enemies] until I am satisfied; my sword will [be like a monster that] [MET, PRS] drinks the blood [of the animals it kills] until it is no longer thirsty. [The enemy soldiers who will be killed] in the north beside the Euphrates River [will be like] [MET] a sacrifice to [me], the Commander of the armies of angels.
Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
11 You people [IDM] of Egypt, go up to the Gilead [region] to obtain medicine; but it will be useless to take all those medicines; you will not be healed.
“Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
12 [People in] the [other] nations will hear how you were humiliated. [People] all over the earth will hear you wailing. [Your mighty] warriors will stumble over each other and they will all fall down together.”
Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
13 [Then] Yahweh gave me this message about King Nebuchadnezzar when he planned to attack Egypt [with his army]:
Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
14 “Shout [this message] throughout Egypt! Proclaim it in Migdol, Memphis, and Tahpenes [cities]! ‘(Get into your positions/Line up) [for the battle]; Prepare to defend yourselves, because [everyone] around you will be killed.’ [PRS, MTY]
“Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
15 Your god is a bull; Why does he fall down? He will not be able to stand up, because Yahweh will knock him down.
Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
16 The soldiers from other countries will stumble and fall over each other, and [then] they will say to each other, ‘Let’s get up and go back to our own people, to our own land. Let’s get away from the swords of our enemies!’
Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
17 There [in Egypt] they will say, ‘The king of Egypt talks loudly, but when our [army] had an opportunity [to defeat our enemies], they failed.’
A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
18 [I, ] the King, who am called the Commander of the armies of angels, say this: ‘As [surely as] I live, someone’s army will be coming [to fight against the army of Egypt]. They will be [extremely powerful], [as though they were as tall] as Tabor Hill, or [as high] as Carmel [Mountain] close to the [Mediterranean] Sea.
“Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
19 [All] you people who live in Egypt, pack your possessions/clothes and prepare to be exiled. Memphis [city] will be destroyed; it will become a ruin, and no one will be living there.
Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
20 Egypt is [like] [SIM] a beautiful young cow, but [the army of a powerful king] from the northeast will come to attack it [like] a horsefly [MET] [bites a cow].
“Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
21 The (mercenaries/soldiers [from other countries] who have been hired) will become like [SIM] fat calves; but they also will turn around and run away; they will not stand [there and fight], because it will be a day when there will be a [great] disaster in Egypt, a day when their people will be [greatly] punished.
Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
22 [The soldiers of] Egypt will run away, as silently as a snake scurries/crawls away. [The army of] the enemy will advance; they will march along carrying their axes like [SIM] men who cut down trees.
Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
23 [I, ] Yahweh, say that they will kill the soldiers [of Egypt] as though [SIM] they were a forest of trees, because the enemy soldiers will be as numerous as [a swarm of] locusts.
Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
24 The people of Egypt will be humiliated; they will be conquered by people from the northeast.’
Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
25 [I, ] the Commander of the armies of angels, the God whom the Israelis [worship], say, ‘I will punish Amon, [the god whom the people] of Thebes [city] worship, and [all] the [other] gods in Egypt. [I will punish] the King of Egypt and [all] those who trust in him.
Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
26 I will cause them to be captured by those who want to kill them—Nebuchadnezzar the King of Babylon, and his army officers. But many years later, people will live in Egypt again. [That will surely happen because] I, Yahweh, have said it.’
Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
27 But you people of Israel who serve me, do not be at all dismayed [DOU] now, because some day I will bring you back from distant places; I will bring your descendants from the land to which they were exiled. [Then you] Israeli people will again live peacefully and safely, and there will not be any [nation] to cause you to be terrified.
“Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
28 [I, ] Yahweh, say to you people of Israel who serve me, ‘Do not be afraid, because I will be with you. I will completely destroy the nations among whom I have scattered you, but I will not completely get rid of you. I will punish you, but I will punish you only as severely as you deserve: It would be wrong if I did not punish you at all.’”
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”

< Jeremiah 46 >