< Jeremiah 37 >

1 After Jehoiakim died, [his son Jehoiachin became king for only three months, after which] King Josiah’s son Zedekiah became the King of Judah. Nebuchadnezzar, the King of Babylon, appointed him to be the new king.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
2 But King Zedekiah and his palace officials and the other people in the land paid no attention to the messages that Yahweh gave me.
Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
3 However, [one day] King Zedekiah sent Jehucal the son of Shelemiah, and Zephaniah the priest, who was the son of Maaseiah, to me. They requested me to pray to Yahweh our God for our [nation].
Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
4 At that time I had not yet been put in prison, so I could come and go wherever and whenever I wanted to, [without being hindered].
To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
5 [At that time], the army of [Hophra], the King of Egypt, came [to the southern border of Judah]. When the army of Babylonia heard about that, they stopped surrounding Jerusalem and left there [to fight against the army from Egypt].
Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
6 Then Yahweh gave this message to me:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
7 “[I], Yahweh, the God whom [you] Israelis [say you belong to], say this: ‘The King of Judah has sent [messengers] to you to ask me [what is going to happen]. Tell the king that even though the army of the King of Egypt came to help him, they are about to return to Egypt.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
8 Then the army of Babylonia will return here and capture this city and burn everything in it.’
Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
9 [So], this is what I say [to you Israelis]: ‘You should not deceive yourselves, thinking that the army from Babylonia has gone and will not return. That is not true.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
10 And even if your soldiers could destroy almost all of the soldiers from Babylonia who are attacking you, and allow only a few of them who were wounded to remain alive in their tents, they would come out [of their tents] and burn this city completely!”’”
Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
11 When the army from Babylonia left Jerusalem because the army from Egypt was approaching,
Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
12 I started to leave the city. I intended to go to the area [where the descendants of] Benjamin live, in order to take possession of my share of the property from my family.
sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
13 But as I was walking out the Benjamin Gate, a guard seized me and said, “You are deserting [us and going] to [the soldiers from] Babylonia!” The man who seized me was Irijah, the son of Shelemiah and grandson of Hananiah.
Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
14 But I [protested and] said, “That is not true! I was not intending to do that!” But Irijah would not pay attention to what I said. He took me to the [king’s] officials.
Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
15 They were very angry with me. They [commanded the guards to] beat me and [then to] put me in the house where Jonathan the king’s secretary stayed. They had changed Jonathan’s house to make it become a prison.
Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
16 They put me in a dungeon/cell in that prison, and I remained there for several days.
Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
17 Then King Zedekiah secretly sent a servant to me, who took me to the palace. There the king asked me, “Do you have any messages from Yahweh?” I replied, “Yes, [the message is that] you will be handed over to the king of Babylon.”
Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
18 Then I asked the king, “What crime have I committed [RHQ] against you or against your officials or against the Israeli people, with the result that you have [commanded that] I be put in a prison?
Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
19 Your prophets predicted that the army of the king of Babylon would not attack you or this land. Why were [RHQ] [their messages] not fulfilled?
Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
20 Your majesty, I plead with you to listen to me. Do not send me back to the dungeon/cell in the house of Jonathan your secretary, because [if you do that, ] I will die there.”
Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
21 So King Zedekiah commanded that [I not be sent back to the prison cell. Instead, ] I was allowed to be watched by the guards in the courtyard [of the palace]. [The king] also [commanded that they should] bring me a loaf of fresh bread every day, until there was no bread left in the city. So [they put me] in that courtyard and I remained there.
Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.

< Jeremiah 37 >