< Jeremiah 27 >

1 Soon after Zedekiah became the King of Judah, Yahweh gave a message to me.
A farkon sarautar Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
2 This is what he said to me: “Make a (yoke/set of wooden bars to fasten around the neck of an ox), but fasten it around your own neck with leather straps.
Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka yi karkiyar itace da maɗaurai ka ɗaura a wuyanka.
3 [Then] send messages to the kings of Edom, Moab, Ammon, Tyre, and Sidon, by telling those messages to the ambassadors from those countries who have come to Jerusalem to [talk to] King Zedekiah.
Sa’an nan ka aika da saƙo zuwa wurin sarakunan Edom, Mowab, Ammon, Taya da Sidon ta bakin jakadu waɗanda suka zo Urushalima wurin Zedekiya sarkin Yahuda.
4 Tell them to give this message to their kings: This is what the Commander of the armies of angels, the God whom the Israeli [people worship, ]:
Ka ba su saƙo wa iyayengijinsu su ce, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ku faɗa wa iyayengijinku wannan.
5 ‘With my very great power [MTY, DOU] I created the earth and the people and the animals that are on the earth. And I can give my power to anyone whom I want to.
Da ikon mai ƙarfi da kuma hannuna da na miƙa na yi duniya da mutanenta da kuma dabbobin da suke ciki, na ba da ita ga duk wanda na ga dama.
6 And now I am going to enable King Nebuchadnezzar of Babylon, who does what I want him to do, to control your countries. I am going to enable him to rule everything, even the wild animals.
Yanzu zan ba da dukan ƙasashenku ga bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon; zan sa namun jeji ma su bauta masa.
7 [The people of] all the nations will work for him, and [later] for his son, and [later] for his grandson, until the time for them [to rule] is finished. Then [the armies of] many great kings from many nations will conquer Babylon.’
Dukan al’ummai za su bauta masa da ɗansa da kuma jikansa har sai har lokacin ƙasarsa ya kai; sa’an nan al’ummai masu yawa da kuma manyan sarakuna za su kasance a ƙarƙashinsa.
8 But now I tell you that you must [do what the king of Babylon wants you to do] [MET], [like an ox that has] a yoke on its neck [must do what its master wants it to do]. I will punish any nation that refuses to do that. I will cause those people to experience war and famine and diseases, until [the armies of] Babylon have conquered that nation.
“‘“Amma fa, duk al’umma ko mulkin da bai bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon ba bai kuwa rusunar da wuyarsa ga karkiyarsa ba, zan hukunta wannan al’umma da takobi, yunwa da annoba, in ji Ubangiji, har sai na hallaka ta ta wurin hannunsa.
9 So, do not pay attention to your [false] prophets and fortune-tellers and people who predict what will happen by working magic or by talking with spirits of dead people. Those people say that the king of Babylon will not conquer your country.
Saboda haka kada ku saurari annabawanku, masu dubanku, masu fassarar mafarkanku, bokayenku ko masu maitancinku waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba.’
10 Those people are [all] liars. [If you believe what they say, ] it will result in your being exiled from your land. I will cause you to be taken from your land, and you will die far away.
Suna muku annabcin ƙaryar ne kawai da za tă kau da ku daga ƙasarku; zan kore ku za ku kuwa hallaka.
11 But the people of any country who do what the King of Babylon wants them to do will remain in their own country and be able to plant their crops [MTY] [as they always have done. That will surely happen because I], Yahweh, have said it.”
Amma duk al’ummar da ta rusuna da wuyarta a ƙarƙashin karkiyar sarkin Babilon ta kuma bauta masa, zan bar al’ummar ta zauna a ƙasarta ta noma ta, ta kuma zauna a can, in ji Ubangiji.”’”
12 [After I gave that message to those ambassadors, ] I gave the same message to King Zedekiah of Judah. [I said to him, ] “If you want to remain alive, do what the King of Babylon and his officials want you to do [MET].
Na ba da wannan saƙo guda ga Zedekiya sarkin Yahuda. Na ce, “Ka rusunar da wuyanka a ƙarƙashin sarkin Babilon; ka bauta masa da kuma mutanensa, za ka kuwa rayu.
13 [It would be foolish for you not to do that, because the result would be that] you and your people would die by [your enemies’] swords or by famine or diseases, which Yahweh will cause any nation to experience that refuses to allow the King of Babylon to rule them.
Me ya sa kai da mutanenka za ku mutu saboda takobi, yunwa da annoba waɗanda Ubangiji ya yi barazana wa duk al’ummar da ba za tă bauta wa sarkin Babilon ba?
14 Do not pay attention to those prophets who say to you, ‘The King of Babylon will not conquer your country.’ They are liars.
Kada ku saurari maganganun annabawa waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba,’ gama annabcin ƙarya suke muku.
15 [This is what] Yahweh says: ‘I have not appointed those prophets. They are saying that I [MTY] gave them messages, but they are lying. So, [if you believe them, ] I will expel you from this land. And you and all those prophets will die [in Babylon]!’”
‘Ban aike su ba,’ in ji Ubangiji. ‘Suna annabcin ƙarya ne da sunana. Saboda haka, zan kore ku za ku kuwa hallaka, da ku da kuma annabawan da suke muku annabci.’”
16 Then I spoke to the priests and the other people, and I said, “This is what Yahweh says: ‘Do not believe your prophets who tell you that all the gold items [that were taken] from my temple [by soldiers from Babylon] will soon be returned from Babylon, because what they are prophesying is a lie.
Sai na ce wa firistoci da dukan waɗannan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku saurari annabawan da suke cewa, ‘Ba daɗewa ba za a komo da kayan gidan Ubangiji daga Babilon.’ Suna muku annabcin ƙarya ne.
17 Do not pay attention to what they say. Surrender to the king of Babylon. If you do that, you will remain alive. [If you do not do that] [RHQ], this entire city will be destroyed.
Kada ku saurare su. Ku bauta wa sarkin Babilon, za ku kuwa rayu. Don me wannan birni zai zama kufai?
18 If they are really prophets who speak messages from me, tell them to plead to me, the Commander of the armies of angels, that [the soldiers from Babylon] will not be allowed to take away to Babylon the valuable items that [still] remain in the temple and in the king’s palace and in [the other palaces in] Jerusalem.
In su annabawa ne da gaske suna kuma da maganar Ubangiji, bari su roƙi Ubangiji Maɗaukaki ya sa kada a kwashe kayayyakin da suka ragu a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da kuma cikin Urushalima a kai Babilon.
19 [I say this] because the [huge] pillars [that are in front of the temple] and the large water tank and the [ten water] carts and all the other items that are used [for offering sacrifices are still in this city].
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da ginshiƙai, kwatarniya, da dakalai, da sauran kayayyaki da aka bar su a birnin nan,
20 King Nebuchadnezzar of Babylon left those things here when he exiled Jehoiachin, the king of Judah, to Babylon, along with all the [other] leaders of Jerusalem and [the leaders of other places in] Judah.
waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe sa’ad da ya kame Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon tare da dukan manyan mutanen Yahuda da Urushalima,
21 [I], the Commander of the armies of angels, the God whom the Israeli [people worship], say this about all those valuable things that are still outside the temple and in the palace of the king of Judah and in [other places in]:
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa game da abubuwan da aka bari a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da Urushalima,
22 They will [all] be carried away to Babylon. And they will stay there until I say that they should be brought back to Jerusalem. Then they will be bought back here. [That is what I, ] Yahweh, say.’”
‘Za a kwashe su zuwa Babilon a can kuwa za su kasance sai ranar da na neme su,’ in ji Ubangiji. ‘Sa’an nan zan komo da su in maido da su wannan wuri.’”

< Jeremiah 27 >