< Jeremiah 25 >
1 After Jehoiakim had been ruling Judah for almost four years, Yahweh gave me this message for all the people of Judah. It was during the year that King Nebuchadnezzar started to rule in Babylon.
Magana ta zo wa Irmiya game da dukan mutanen Yahuda a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wadda ta kasance shekara ta fari ta Nebukadnezzar sarkin Babilon.
2 I spoke this message to all the people in Jerusalem and [other places in] Judah:
Saboda haka Irmiya annabi ya ce wa dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima.
3 “Yahweh has been giving me messages for 23 years. He started giving me messages when Josiah, the son of Amon, had been ruling Judah for almost 13 years. And I have faithfully told you those messages, but you have not paid any attention to them.
Shekaru ashirin da uku, daga shekara ta goma sha uku ta Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda har zuwa wannan rana, maganar Ubangiji ta zo mini na kuma yi muku magana sau da sau, amma ba ku saurara ba.
4 Many times Yahweh has sent to you the prophets who served him, but you have not listened to them or paid any attention to what they said.
Ko da yake Ubangiji ya aika dukan bayinsa annabawa gare ku sau da sau, ba ku saurara ba, ba ku kuma kula ba.
5 Each time their message was this: ‘Turn from all your evil behavior [MET], from all the evil things that you have continually been doing. If you do that, you will be able to stay in this land that Yahweh gave to you and to your ancestors, [to belong to you] forever.
Sun ce, “Ku juye yanzu, kowannenku, daga mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa iya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku da kuma kakanninku har abada abadin.
6 Do not cause Yahweh to become angry by serving and worshiping idols that you have made with your hands. If you do not cause him to be angry, he will not punish/harm you.’
Kada ku bi waɗansu alloli don ku bauta ku kuma yi musu sujada; kada ku tsokane ni in yi fushi da abin da hannuwanku suka yi. Sa’an nan ba zan kawo muku lahani ba.”
7 And Yahweh says, ‘But you would not pay attention to the messages that I [gave to those prophets]. You caused me to become extremely angry by [your worshiping idols] that you had made with your own hands. That resulted in my punishing you.
“Amma ba ku saurare ni ba,” in ji Ubangiji, “kun tsokane ni da abin da kuka yi da hannuwanku, kuka kuma kawo lahani wa kanku.”
8 So [now, I], the Commander of the armies of angels, say that because you have not paid attention to what I said,
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Domin kun ƙi ku saurara ga maganata,
9 I will gather all [the armies of] the nations that will come from the northeast. I have appointed King Nebuchadnezzar of Babylon to lead them. I have appointed him to do my work for me. I will bring those [armies] to attack this land and nearby countries. I will completely destroy them, and cause them to be places that people are horrified about, and that people will (ridicule/act contemptuously toward), places that will be ruined forever.
zan kira dukan mutanen arewa da bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon,” in ji Ubangiji, “zan kuma kawo su su yi gāba da wannan ƙasa da mazaunanta da kuma gāba da dukan al’ummai da suke kewaye. Zan hallaka su sarai in kuma mai da su abin bantsoro da abin dariya, za su kuma zama kufai har abada.
10 I will cause happy singing and laughing to cease in your land. There will no longer be brides and bridegrooms talking [joyfully]. There will not be the sound of people grinding [grain] with millstones. There will be no lamps lit [in your houses].
Zan kawar da muryoyin farin ciki da murna daga gare su, muryoyin amarya da na ango, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.
11 All of this land will become a desert where no one will live. And [the people of] Israel and of the nearby countries will [will be exiled to Babylonia and] (work for/be slaves of) the kings of Babylon for seventy years.
Dukan wannan ƙasa za tă zama kango, kuma waɗannan al’ummai za su bauta wa sarkin Babilon shekaru saba’in.
12 Then, after [they have been in Babylonia for] seventy years, I will punish the King of Babylonia and his people for the sins that they have committed. I will cause Babylonia to become a wasteland/desert forever.
“Amma sa’ad da shekaru saba’in ɗin suka cika, zan hukunta sarkin Babilon da kuma al’ummarsa, ƙasar Babiloniyawa, saboda laifinsu,” in ji Ubangiji, “in kuma mai da ita kango har abada.
13 I will cause them to experience all the terrible things that Jeremiah has written about—all the punishments that he predicted will happen to all those nations.
Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abubuwan na yi magana a kanta, dukan abubuwan da aka rubuta a wannan littafi, abubuwan da Irmiya kuma ya yi annabci a kan dukan al’ummai.
14 The leaders of many nations will cause the people of Babylonia to become their slaves, like the people of Babylonia caused my people to become slaves. I will punish them like they deserve for [having caused my people to suffer].’”
Su kansu al’ummai da sarakuna masu yawa za su bautar da su; zan sāka musu bisa ga ayyukansu da aikin hannuwansu.”
15 Then Yahweh, the God [we] Israelis [worship], gave me [a vision. In the vision he was holding a cup of wine]. He said, “Take from me this cup that is full of [wine that represents] punishment [MTY]. I will cause all [the leaders of] the nations to which I will send you to drink [some of] the wine in this cup.
Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa mini, “Ka karɓi kwaf ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.
16 When they drink [the wine], they will stagger and act like crazy people, because [they will realize that] I will (massacre many of their people/cause many of their people to be killed) [MTY] with swords.”
Sa’ad da suka sha, za su yi ta tangaɗi su kuma yi hauka saboda takobin da zan aika a cikinsu.”
17 So, [in the vision, ] I took that cup [full of wine] from Yahweh, and I took it to all the nations to which he sent me, and caused [the leaders of those] nations to drink [some of that wine].
Saboda haka na karɓi kwaf daga hannun Ubangiji na sa dukan al’ummai waɗanda ya aiko ni wurinsu su sha.
18 [I went to] Jerusalem and the [other] towns in Judah, and the king and [the other] officials drank [some of the wine] from that cup. And, starting from that day, they all [eventually] were removed from having authority, and became [people whom others] (ridiculed/acted contemptuously towards), who were despised, and cursed.
Urushalima da garuruwan Yahuda, sarakunan da fadawanta, don su mai da su kufai da kuma abin bantsoro da ba’a da la’ana, yadda suke a yau;
19 [In the vision I went to] Egypt [and gave some of the wine] to the king and his officials and many of his people,
Fir’auna sarkin Masar, ma’aikatansa, fadawansa da dukan mutanensa,
20 and to foreigners who were living there. [In the vision I also went to] Uz land and to Ashkelon, Gaza, Ekron, and Ashdod [cities and gave some of the wine] to the kings [of those places].
da dukan baƙin da suke can; dukan sarakunan Uz; dukan sarakunan Filistiyawa (waɗannan na Ashkelon, Gaza, Ekron da mutanen da aka bari a Ashdod);
21 [Then in the vision I went to the] Edom, Moab, and Ammon [people-groups],
Edom, Mowab da Ammon;
22 and to Tyre and Sidon [cities] and to areas across the [Mediterranean] Sea, and [gave some of the wine] to the kings [of those places].
dukan sarakunan Taya da Sidon; sarakunan bakin teku a ƙetaren teku;
23 [In the vision I then went] to Dedan, Tema, and Buz [cities in Arabia] and to other distant places (OR, places where people cut their hair short), [and gave some of the wine to leaders in those areas].
Dedan, Tema, Buz da dukan waɗanda suke a manisantan wurare;
24 [In the vision I also went to other places in] Arabia and to the [kings of tribes] in the desert
dukan sarakunan Arabiya da dukan sarakunan baƙin da suke zama a hamada;
25 and to the kings of the Zimri, Elam, and Media [people-groups],
dukan sarakunan Zimri, Elam da Mediya;
26 and to kings in countries to the north that are near [to Israel] and to countries that are far [from Israel], one after the other— [I went to] all the kingdoms in the world [HYP]. And finally, [in my vision I went to] Babylon, and gave [some of] the wine to the king of Babylon—the wine [that symbolized that Yahweh would punish the people of Babylon because he was angry with them] [MTY].
da kuma dukan sarakunan arewa, nesa da kuma kusa, bi da bi, dukan mulkokin duniya. Bayan dukansu kuma, sai sarkin Sheshak ma yă sha.
27 Then [in the vision Yahweh said to me], “Tell them that this is what the Commander of the armies of angels, the God whom we Israelis [worship], says: ‘Drink [from this cup some of the wine that represents the punishment that I will give you]. Drink [a lot of it] and become drunk and vomit. You will fall down and not get up again, because I will cause you to be killed in wars [MTY] that I will send to you.
“Sa’an nan na faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku sha, ku bugu ku kuma yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku ƙara tashi saboda takobin da zan aiko muku.’
28 If any of those to whom you give this wine [MTY] refuse to drink it, tell them that the Commander of the armies of angels says that they must drink it.
Amma in suka ki su karɓi kwaf ɗin daga hannunka su sha, ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa dole ku sha!
29 I am starting to cause the people of my own city to experience disaster. [Do you think that] you should not be punished [RHQ]? No, you will surely be punished [LIT] because I am causing there to be wars in all the nations on the earth. [That will surely happen because] I, the Commander of the armies of angels, have said it.’
Ga shi, na sa masifa tă yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana, kuna gani za ku tafi ba hukunci? Ba za ku tafi ba hukunci ba, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
30 Now tell them all those things that I have said, and also say this to them: ‘Yahweh will [shout to them] from his holy dwelling [in heaven] [MTY] and [it will sound like] the roar of a lion. He will shout like [SIM] people shout when they are treading on grapes [to make juice for wine]; he will shout to everyone on the earth.
“Yanzu ka yi annabcin dukan waɗannan maganganu a kansu ka kuma ce musu, “‘Ubangiji zai yi ruri daga bisa; zai yi tsawa daga mazauninsa mai tsarki ya kuma yi ruri da ƙarfi a kan ƙasarsa. Zai yi ihu kamar waɗanda suke matsin’ya’yan inabi, yi ihu a kan dukan waɗanda suke zaune a duniya.
31 Even people in very remote places around the earth will hear him shouting, because he will say why he will judge and punish all the nations. He will cause the wicked people to be slaughtered with swords. [That will surely happen because] Yahweh has said it.’
Hayaniya za tă taso har iyakar duniya, gama Ubangiji zai kawo tuhume-tuhume a kan al’ummai; zai kawo shari’a a kan dukan’yan adam ya kuma kashe mugaye da takobi,’” in ji Ubangiji.
32 Then tell them that this is what the Commander of the armies of angels says: ‘Listen to this! There will be disasters in one nation after another. [I am preparing to punish them like] [MET] a great storm that starts in the most distant places on the earth.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Duba! Masifa tana yaɗuwa daga al’umma zuwa al’umma; hadari mai girma yana tasowa daga iyakar duniya.”
33 When that happens, [the corpses of] those whom I have [caused to be] slaughtered will fill the earth from the east to the west. And no one will mourn for them, and no one will gather their corpses to bury them. They will be [scattered] on the ground like manure.
A lokacin waɗanda Ubangiji ya kashe za su kasance a ko’ina, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi kuka dominsu, ba za a tattara su don a binne ba, amma za su zama kamar juji da an tsiba a ƙasa.
34 You [evil] leaders, weep and moan! You who should take care of my people, [fall down and] roll in the dust/dirt. It is time for you to be slaughtered; you will fall down and be shattered like a fragile vase [shatters when it falls to the ground].
Ku yi kuka ku kuma yi makoki, ku makiyaya; ku yi ta birgima a ƙura, ku shugabannin garke. Gama lokacin da za a yanka ku ya zo; za ku fāɗi ku kuma farfasa kamar tukunyar yumɓu mai kyau.
35 You will not find any place to hide, there will be no place to which you can escape.
Makiyaya ba za su sami wurin da za su gudu su tafi ba, shugabannin garke ba za su sami wurin kuɓuta ba.
36 [People will] listen to your leaders crying when [I], Yahweh, am ruining your nation.
Ji kukan makiyaya, kururuwan shugabannin garke, gama Ubangiji yana hallaka wurin kiwo.
37 Your peaceful meadows will become a wasteland/desert because I will be extremely angry.
Rafi mai gudu a hankali zai zama kango saboda zafin fushin Ubangiji.
38 I will leave [my dwelling like] [SIM] a lion leaves its den [to attack other animals], and I will cause your land to become desolate when I, because I am very angry [with you], cause [your enemies to slaughter you with their] swords.’”
Kamar zaki zai bar wurin ɓuyarsa, ƙasarsu kuma za tă zama kufai saboda takobin masu danniya da kuma saboda zafin fushin Ubangiji.