< Jeremiah 22 >

1 This is another message that Yahweh gave [to me]: “Go down to the palace of the king of Judah and say this to him:
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
2 ‘You are the king of Judah. You are the ruler [MTY], like King David was. You and your officials and your people must listen
‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
3 to what Yahweh says: “Act fairly and justly. Do what is right. Help those who have been robbed. Rescue people from those who oppress them. Stop doing evil things. Do not mistreat those who have come here from other countries, and do not mistreat orphans and widows. Stop murdering here [in Jerusalem] [MTY] those who (are innocent/have not done things that are wrong).
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
4 If you obey those commands carefully, there will [always] be some descendant of King David who will be ruling here [MTY] [in Jerusalem]. The king and his officials and other people will ride through the gates of the city in chariots and on horses.
Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
5 But if you refuse to pay attention to those commands, I, Yahweh, solemnly declare, with myself [MTY] as a witness, that this palace will become a pile of rubble.”’”
Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
6 And this is what Yahweh says about the king’s palace: “[I like] this palace, like I like the forests in the Gilead [region] and the mountains in Lebanon. But I will cause this palace to become a desert, a place that no one lives in.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
7 I will summon enemy troops who will destroy this palace; each of their soldiers will use his own tools [to wreck the building]. They will cut into pieces the beautiful big cedar [beams] and throw them into a fire.”
Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
8 People from many nations will walk past [the ruins of] this city and say to each other, “Why did Yahweh destroy this city that was [very] great?”
“Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
9 And [other] people will reply, “[He did it] because his people stopped obeying the agreement that they had made with Yahweh their God. Instead, they worshiped [DOU] other gods.”
Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
10 [Yahweh also says, ] “Do not mourn for King [Josiah]; do not cry because he has died. Instead, mourn for [King Jehoahaz, his son], [because] he will be captured and taken to another country, and he will never return to see his own country, [Judah], again.”
Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
11 Jehoahaz became king after his father, King Josiah, [died], but Jehoahaz indeed was captured and taken [to Babylonia]. And this is what Yahweh says about him: “He also will never return [to Judah].
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
12 He will die in that far-away country and will never see his own country again.”
Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
13 [And Yahweh said to me], “Terrible things will happen to [King Jehoahaz’s brother, King Jehoiakim]. He unjustly [forced men to] build his palace. The rooms on the upper level were built [by men who were forced] unjustly [to do that work]; he forced his neighbors to work for nothing; he did not pay them anything.
“Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
14 He said, ‘I will [force my workers to] build a huge beautiful palace with very large rooms and [many] windows. They will cover the walls with [fragrant] cedar panels/timber and paint them bright red.’”
Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
15 But it is certainly not [RHQ] having a beautiful cedar palace that causes a king to be great! Jehoiakim’s father, Josiah, also had [RHQ] plenty of things to eat and drink. But Josiah always did things that are right and just, and that is why God blessed him.
“Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
16 Josiah acted justly/fairly and helped poor and needy people, so things went well for him. Yahweh says, “That is [RHQ] the way a person should behave who knows me.
Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
17 But [Jehoiakim], you [MTY] are greedy and desire only to obtain things by acting dishonestly. You murder [MTY] innocent people, you oppress poor people, and you treat people cruelly and violently.”
“Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
18 Therefore, this is what Yahweh says about Jehoiakim, the son of King Josiah: “[When he dies], people will not mourn for him. They will not say to each other, ‘It is very sad; we are so sorry!’ The people whom he ruled will not mourn for him, saying, ‘We are sad that our king is dead; we are so sorry that the wonderful things [that happened while he was king are ended].’
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
19 [When he dies, people will do to] his corpse what they do to a dead donkey; his [corpse] will be dragged out of Jerusalem and dumped outside the gates!
Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
20 [You people of Judah], go to [the mountains in] Lebanon and weep, shout in the [mountains of the] Bashan [region], cry out in [the mountains of] Moab, because all your friends [in those areas] have been destroyed.
“Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
21 When you were prosperous, I warned you, but you replied, ‘We will not pay attention [to what you say].’ You have been acting like that since you were young; you have never obeyed me.
Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
22 [So, now I will punish] all your leaders; [it will be as though] they have been blown away by the wind. They will be captured [by your enemies] and taken to another country. When that happens, you will [truly] be ashamed and disgraced because of all the wicked things [that you have done].
Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
23 [Now, your king] enjoys living in the cedar rooms in his palace, but [soon] he will be punished, and then he will groan like [SIM] a woman who is giving birth to a baby.”
Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
24 Yahweh says this: “Jehoiachin, son of King Jehoiakim of Judah, as surely as I am alive, [I will punish you]. Even if you were the ring on my finger that shows that I am the king, I would pull you off.
“Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
25 You are afraid of King Nebuchadnezzar of Babylon and his huge army, [because] they are wanting to kill you. I will enable them to capture you.
Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
26 I will expel you and your mother [from this land], and you will be taken to another country. Neither of you was born there, but you will both die there.
Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
27 You will never return to this land that you will very much desire to return to.”
Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
28 [Someone said, ] “Jehoiachin will be [RHQ] like a broken pot that is despised and which no one wants. He and his children will be (exiled/forced to go) to a foreign land.
Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
29 [I want] the people in this land to listen carefully to this message from Yahweh.”
Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
30 This is what Yahweh says: “[In the record about the kings of Judah, ] write down that [it will be as though] this man [Jehoiachin] had no children, and that he has not been successful during his life, because none of his children/descendants will [ever] become king to rule over [the people of] Judah.”
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”

< Jeremiah 22 >