< Jeremiah 2 >

1 Yahweh gave me another message
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 [to proclaim to everyone in Jerusalem. He said that I should tell them this] [MET]: “I, Yahweh, remember that you very much wanted to please me [long ago]. [You tried to please me like] a bride [tries to please her husband]; You loved me, and you followed me through the desert [DOU].
“Tafi ka yi shela a kunnuwar Urushalima cewa, “‘Na tuna da amincin ƙuruciyarki, yadda kamar amarya kika ƙaunace ni kika kuma bi ni cikin hamada, cikin ƙasar da ba a yi shuka ba.
3 [At that time you] Israelis (were set apart/belonged only) to me; [you belonged to me like] the first part of the harvests belong to me [MET]. I promised to punish all those who harmed you, my people, and truly I did send disasters on them. [That happened because I], Yahweh, said [that it would happen].”
Isra’ila tsattsarka ce ga Ubangiji, nunan fari na girbinsa; dukan waɗanda suka cinye ta an same su da laifi, masifa kuwa ta same su,’” in ji Ubangiji.
4 So, you [descendants of] [MTY] Jacob, all you people of [MTY] Israel,
Ka saurari maganar Ubangiji, ya gidan Yaƙub, dukanku zuriyar gidan Isra’ila.
5 listen to what Yahweh says: “(What sin did I commit [RHQ] that caused your ancestors to turn far away from me?/Though your ancestors found no fault in me, they turned far away from me.) They worshiped worthless idols, and they themselves became worthless.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Wane laifi ne kakanninku sun same ni da shi, da suka tsaya nesa da ni? Sun bi gumakan banza su kansu suka kuma zama banza da kansu.
6 They did not say, ‘Yahweh brought us [safely] out of Egypt, and he led us through a desert where there were a lot of pits; he led us where there was no water and where it was very dangerous, through a land where no one lives, and no one even travels. (So where is Yahweh now?/So he should be helping us now!) [RHQ]’
Ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji, wanda ya fitar da su daga Masar ya bishe su cikin jeji cikin hamada da kwazazzabai ƙasa mai fări da kuma duhu, ƙasar da ba kowa mai ratsa ta ba kowa kuma mai zama a cikinta?’
7 And when I brought you into a very fertile land, in order that you could enjoy [all] the fruit and [other] good things that you would harvest, you caused the land that I promised to give to you to be unfit for me and to become disgusting/detestable to me.
Na kawo ku zuwa ƙasa mai albarka don ku ci amfaninta da abubuwa masu yalwar da take bayarwa. Amma kuka zo kuka ƙazantar da ƙasata kuka kuma mai da gādona abin ƙyama.
8 [Your] priests also did not say, ‘(Where is Yahweh now?/Yahweh should be helping us now!)’ [RHQ] Those who teach/explain my laws do not [want to] know me, and [your] leaders have rebelled against me. [Your] prophets gave you messages from [their god] Baal, and they worship worthless idols.”
Firistoci ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji ba.’ Waɗanda suke amfani da doka ba su san ni ba; shugabanni suka yi mini tawaye. Annabawa suka yi annabci ta wurin Ba’al, suna bin gumakan banza.
9 “So, I will accuse you in court. [In future years], I will say what your children and your grandchildren have done that is wrong. [That will happen because I], Yahweh, have said [that it will happen].
“Saboda haka ina sāke tuhumarku,” in ji Ubangiji. “Zan kuma tuhumi’ya’ya’ya’yanku.
10 If you go [west] to the island of Cyprus, or if you go [east] to Kedar [land, ] and if you ask people in those places, they will tell you that no people [from their countries] have ever done the wicked things that you people have done!
Ku ƙetare zuwa tsibiran Kittim ku gani, ku aika zuwa Kedar ku duba da kyau; ku ga ko an taɓa yin wani abu haka.
11 The people of no other nation have ever [RHQ] abandoned their gods that they thought were glorious and started to worship gods that are not really gods, but you people have abandoned me, your glorious God, and are worshiping gods that are useless.
Akwai wata al’ummar da ta canja allolinta? (Duk da haka su ba alloli ba ne sam.) Amma mutanena sun musayar da ɗaukakarsu da gumakan banza.
12 [It is as though everything in] the sky is surprised and dismayed/appalled [about what you have done]; [it is as though] they tremble because they are very horrified.
Ku girgiza saboda wannan, ya sammai, ku kuma razana don tsoro mai girma,” in ji Ubangiji.
13 [You], my people, have done two evil things: You have rejected me, the one who is [like] [MET] a fountain [where you can obtain] fresh water, and you [are worshiping gods that are like] [MET] pits in the ground that are cracked and which are not able to hold any water.
“Mutanena sun aikata zunubai guda biyu. Sun rabu da ni, ni da nake maɓulɓular ruwan rai, sun kuma haƙa tankunan ruwansu, tankuna ruwan da suka fashe da ba za su iya riƙe ruwa ba.
14 You Israeli people, you were certainly not [RHQ] slaves when you were born; you were captured [by your enemies].
Isra’ila bawa ne, bawa ne ta wurin haihuwa? Me ya sa ya zama ganima?
15 [Your enemies] [MET] roared [like] lions, and they destroyed your land. [Now] your towns have been burned, and no one lives in them.
Zakoki sun yi ruri; sun yi masa ruri. Sun lalatar da ƙasarsa; an ƙone garuruwansa aka kuma watse daga ciki.
16 Soldiers from Memphis and Tahpenes, [cities in Egypt], have [defeated you] [and] shaved your heads [to show that you are their slaves].
Haka ma, mutanen Memfis da Tafanes sun aske rawanin kanka
17 But it is [RHQ] because you abandoned [me], Yahweh, that these disasters have happened to you.
Ba kai ne ba ka jawo wa kanka ba ta wurin rabuwa da Ubangiji Allahnka sa’ad da ya bi da kai a hanya?
18 So (why are you trying to make an alliance with [MET] the rulers of Egypt?/it certainly will not help you to make an alliance with the rulers of Egypt) [RHQ]. Why are you trying to make an alliance with [MET] the rulers of Assyria who live near the [Euphrates] River?
To, me ya sa za ka Masar don shan ruwa daga Shihor? Kuma me ya sa za ka Assuriya don shan ruwa daga Kogi?
19 [It is because] you have been [very] wicked that I [PRS] will punish you. It is because you have turned away from me that I [PRS] will condemn you. [When I do that], you will realize that painful and evil [DOU] things will happen to you because you have forsaken [me], Yahweh, your God, and you no [longer] revere me. [That will certainly happen because] I, Yahweh, the Commander of the armies of angels in heaven, have said it.
Muguntarka za tă hukunta ka; jan bayanka zai tsawata maka. Sai ka lura ka kuma gane yaya mugu da kuma ɗaci suke a gare ka sa’ad da ka rabu da Ubangiji Allahnka kuma ba ka tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
20 Long ago, you stopped obeying [me] [MET], and you would not allow [me] to lead you [MET]; you refused to worship [me]. Instead, you worship idols that are under trees on the top of every hill, and your young women have sex with [EUP] [men at those places].
“Tun da daɗewa ka karya karkiyarka ka kuma tsintsinke sarƙoƙinka; sai ka ce, ‘Ba zan bauta maka ba!’ Tabbatacce, a kan kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane ɗanyen itace ka kwanta kamar karuwa.
21 [It is as though] [MET] you were a grapevine that I planted when it was a cutting from a very good vine. So now it is disgusting that [RHQ] you have become [like] a rotten worthless vine.
Na shuka ka kamar zaɓaɓɓen inabi iri mai kyau da kuma wanda za a dogara a kai. Yaya kuma ka juya kana gāba da ni ka lalace, ka zama inabin jeji?
22 Your guilt from your sins is like [MET] very bad stains on a cloth, and you cannot get rid of those stains even by using very strong soap. [This is true because I], Yahweh, have said it.
Ko da yake ka wanke kanka da sabulu ka yi amfani da sabulu mai yawa, duk da haka har yanzu tabon laifinka yana nan a gabana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
23 You say that you have not sinned. You say ‘We have not become unacceptable to God; we have not worshiped Baal.’ But think about [the disgusting things that you do very eagerly] in [Hinnom] Valley [outside Jerusalem]. You are like desperate female camels, running here and there [to find male camels to have sex with].
“Yaya za ka ce, ‘Ban ƙazantu ba; ban bi Ba’al ba’? Duba yadda ka yi a cikin kwari; ka ga abin da ka yi. Kai kamar makwaɗaciyar raƙuma ce mai zafin gudu kana gudu nan da can,
24 You are [like] wild female donkeys in the desert. They sniff the air to find where the male donkeys are, and no one can [RHQ] restrain them. The male donkeys that want them do not become tired searching for them, because at mating time they find them [easily].
kamar jakar jejin da ta saba da hamada, mai busar iska cikin son barbaranta sa’ad da take son barbara wa zai iya hana ta? Jakin da yake nemanta, ba ya bukatar wahalar da kansa; a lokacin barbara za a same ta.
25 You constantly run here and there [to find idols to worship], with the result that your sandals are worn out, and your throats have become dry. [I told you to stop doing that], but you said, ‘We cannot stop, because we love foreign gods, and we must worship them.’”
Kada ka yi gudu har ƙafafunka su zama ba takalma maƙogwaronka kuma ya bushe. Amma sai ka ce, ‘Ba amfani! Ina ƙaunar baƙin alloli kuma dole in bi su.’
26 [Yahweh says this]: “A robber is disgraced when he is caught. And all of you, including your kings and priests and prophets, are similarly disgraced.
“Kamar yadda akan kunyatar da ɓarawo sa’ad da aka kama shi, haka gidan Isra’ila zai sha kunya, su, sarakunansu da shugabanninsu, firistocinsu da kuma annabawansu.
27 You say to [a piece of] wood [that is carved to become a sacred idol], ‘You are our father!’ And you say to a stone [that you have set up], ‘You are our mother!’ You have rejected [IDM] me, but when you experience troubles, you cry out to me to rescue you.
Kuna ce wa itace, ‘Kai ne mahaifina,’ ga dutse kuma, ‘Kai ne ka haife ni.’ Sun juye mini bayansu ba fuskokinsu ba; duk da haka sa’ad da suna cikin wahala, sukan ce, ‘Zo ka cece mu!’
28 Why do you not [RHQ] cry out to the gods that you made? You have as many gods as you have cities [and towns] in Judah. So why do you not plead with them to rescue you when you experience disasters?
To ina allolin da kuka yi wa kanku? Bari su zo in suna iya cetonku sa’ad da kuke cikin wahala! Gama kuna da alloli masu yawa kamar yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda.
29 You complain that it was wrong for me [not to have rescued you], but you have all rebelled against me.
“Me ya sa kuke tuhumana? Dukanku kun yi mini tawaye,” in ji Ubangiji.
30 I punished some of you, but you did not learn anything from my doing that. You have killed many of the prophets that I [sent to you], like [SIM] fierce lions kill [other animals].
“A banza na hukunta mutanenku; ba su yi gyara ba. Takobinku ya cinye annabawanku kamar zaki mai jin yunwa.
31 You people of Israel, pay attention to what I say. I have certainly [RHQ] never [abandoned you] in a desert; I have never [left you] in a land full of darkness. So, why do you, my people, say ‘We are free from God’s control; we will not return to [worship] God any more’?
“Ku na wannan zamani, ku saurari maganar Ubangiji. “Na zama wa Isra’ila hamada ne ko ƙasa mai babban duhu? Me ya sa mutanena suke cewa, ‘Muna da’yanci mu yi ta yawo; ba za mu ƙara zuwa wurinka ba’?
32 A young woman would certainly never [RHQ] forget [to wear] her jewelry, and a bride would never [RHQ] forget to wear her wedding dress, but you my people have forgotten me for many years.
Budurwa za tă manta da kayan adonta amarya ta manta da kayan adon aurenta? Duk da haka mutanena sun manta da ni, kwanaki ba iyaka.
33 You know how to easily find [gods from other countries] whom you can love. You can find them as easily as a prostitute [can find men to sleep with].
Kuna da azanci sosai a bin masoya! Kai, ko mafiya muni cikin mata tana iya koya daga hanyoyinku.
34 Although you have on your clothes the blood of poor people whom you have murdered, people who (were innocent/had not done things that are wrong),
A rigunanku mutane kan sami jinin matalauta marasa laifi, ko da yake ba ku kama su suna fasawa su shiga ba. Duk da haka
35 you say ‘We have not done anything that is wrong; so surely [Yahweh] is not angry with us.’ But I will punish [MTY] you [severely] for saying ‘We have not sinned.’
kuna cewa, ‘Ba ni da laifi; ba ya fushi da ni.’ Amma zan zartar da hukunci a kanku domin kun ce, ‘Ban yi zunubi ba.’
36 Previously you requested [the army of] Assyria to help you, but they were not able to help you. Now you have requested [the army of] Egypt to help you, but they will not be able to help you, either.
Don me kuke yawo da yawa haka, kuna ta canjin hanyoyinku? Masar za tă kunyata ku yadda kuka sha kunya a wurin Assuriya.
37 They will capture you, and you will be [their prisoners] [MTY], led to Egypt, [very ashamed] with your hands on your heads. That will happen because I, Yahweh, have rejected those [nations] that you are relying on, and they will not be able to help you at all.”
Za ku kuma bar wurin da hannuwanku a kanku, gama Ubangiji ya ƙi waɗanda kuka amince da su; ba za ku zama abin taimako a gare su ba.

< Jeremiah 2 >