< Isaiah 9 >

1 However, those in Judah who have been distressed/worried will not [continue to] suffer. Previously, Yahweh humbled [the people in] the land [where the tribes of] Zebulun and Naphtali [live]. But in the future he will honor [the people who live in] that Galilee region, along the road between the Jordan [River] and the [Mediterranean] Sea, where [many] foreigners live.
Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
2 [Some day, it will be as though] [MET] the people who walked in darkness will see a great light. A [great] light will shine on those who live in a land where they have great troubles/distress.
Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
3 [Yahweh], you will cause us people in Israel to rejoice; we will become very happy. We will rejoice about what you [have done] like [SIM] people rejoice when they harvest their crops, [or] like soldiers rejoice when they divide up among themselves the things that they have captured in a battle.
Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
4 You will cause us to no longer be slaves [MET] [of those who captured us]; you will lift the heavy burdens from our shoulders. [It will be as though] you will break the rods of those who oppressed us, like you did when you destroyed [the army of] the Midian people-group.
Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
5 The boots that the enemy soldiers have worn and their clothing which has stains of blood on them will all be burned up; they will only be fuel for a [big] fire.
Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
6 Another reason that we will rejoice is that a [special] child will be born for us; [a woman will give birth to] a son, who will be our ruler. And his names will be ‘Wonderful Counselor’, ‘Mighty/Powerful God’, ‘[Our] Everlasting Father’, and ‘Prince/Ruler [who enables us to have] Peace’.
Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
7 His rule, and the peace that he [brings/causes], will never end. He will rule [MTY] fairly and justly [DOU], like [his ancestor King] David did. This will happen because the Commander of the armies of angels greatly desires that it happen.
Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
8 The Lord has warned the people of Israel, the descendants of Jacob; he has said that [he will punish] them.
Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
9 And all the people in Samaria and [other places in] Israel know that, [but] they are very proud and arrogant [DOU]. They say, “Our city has been destroyed, but we will [take away the broken bricks from the ruins] [and] replace them with carefully cut stones. Our sycamore-fig trees have been cut down [by our enemies], but we will plant cedar trees [in their place].”
Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
“Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
11 But Yahweh brought the armies of [Assyria], the enemies of King Rezin [of Syria, to fight] against Israel and incited [other] nations [to attack Israel].
Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
12 [The army of] Syria [came] from the east, and [the army of] Philistia [came] from the west, and they destroyed Israel [like a wild animal tears another animal apart and] [MET] devours it. But even after that happened, Yahweh was still very angry with them. He was ready to strike them with his fist again.
Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
13 [But even though] Yahweh punished his people [like that], they [still] did not return to him [and worship him]. They [still] did not request the Commander of the armies of angels [to assist them].
Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
14 Therefore, in one day Yahweh will get rid of [those who are like] Israel’s head and [those who are like] its tail; the [ones who are like] the top of the palm tree and the [ones who are like] the bottom.
Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
15 The leaders [DOU] of Israel are the head, and the prophets who tell lies are the tail.
dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
16 The leaders of the people have misled them; they have caused the people that they are ruling to be confused.
Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
17 For that reason, Yahweh is not pleased with the young men [of Israel], and he does not [even] act mercifully toward the widows and orphans, because they are all ungodly and wicked, and they all say things that are foolish. [But] Yahweh still is angry with them; he is ready to strike them with his fist again.
Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
18 When people do wicked things, it is like [SIM] a brushfire [that spreads rapidly]. It burns up [not only] briers and thorns; it starts a big fire in the forests from which clouds of smoke will rise.
Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
19 [It is as though] the [whole] land is burned [black] because the Commander of the armies of angels is extremely angry with the Israeli people. They will become like [SIM] fuel for that great fire, and no one will try to rescue even his [own] brother [from that fire].
Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
20 Israeli people will attack their neighbors on the right [to get food from them], but they will still be hungry. They will [kill those who live in houses] on the left and eat their flesh, but their stomachs will still not be full.
A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
21 [People of the tribes of] Manasseh and Ephraim will attack each other, and [then] they will both attack the people of Judah. But even after that happens, Yahweh will still be very angry with them. He will be ready to strike them with his fist again.
Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.

< Isaiah 9 >