< Isaiah 8 >

1 Then Yahweh said to me, “Make a large signboard. And write clearly on it, ‘Maher-Shalal-Hash-Baz’ [which means ‘quickly (plunder/take by force) and steal everything’].”
Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
2 [So] I requested Uriah the [Supreme] Priest and Jeberekiah’s son Zechariah, men who were both honest/trustworthy witnesses, to watch me as I was doing that.
Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
3 Then I had sex with [EUP] [my wife, who was] a prophetess, and she became pregnant and [then] gave birth to a son. Then Yahweh said to me, “Give him the name Maher-Shalal-Hash-Baz (which means ‘suddenly attacked, quickly conquered’),
Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
4 because before he is old enough to say ‘papa’ or ‘mama’, the King of Assyria will [come with his army and] quickly take away all the valuable things in Damascus and in Samaria.”
Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
5 Yahweh spoke to me again and said, “[Tell the people of Judah, ]
Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
6 ‘[I have taken good care of] you people, but you have rejected that, [thinking that] my help was very little, like [MET] the little canal through which water flows from the Gihon Spring into Jerusalem. Instead, you have been happy [to request help from] King Rezin and King Pekah.
“Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
7 Therefore, I will cause the people of Judah to be attacked by [the powerful army of] the King of Assyria, which will be [like] a great flood from the [Euphrates] River. Their soldiers will [be everywhere in your country, like] a river that overflows all its banks.
saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
8 Those soldiers will go all over Judah— [like a river whose water] [MET] rises as high as a person’s neck. Their army will spread over the land [quickly], like an eagle, and they will cover your entire land! But I will be with you!’”
Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
9 Listen, all you [people in] distant countries! [You can] prepare to attack Judah. [You can] prepare [for battle, and shout your] war-cries, but your [armies will] be crushed/shattered!
Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
10 [You can] prepare for what you will do [to attack Judah], but what you plan to do will not happen! You will not succeed, because God is with us!
Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
11 Yahweh strongly warned me [MTY] not to act like the [other] people in Judah did. He said to me,
Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
12 “Do not say that everything that people do is conspiring/rebelling [against the government], like [other] people say, and do not (be afraid of/worry about) the things that other people are afraid of.
“Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
13 [I, ] the Commander of the armies of angels, am the one you should consider to be holy. And I am the one you should fear, the one you should revere.
Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
14 I will protect you(sg). [But as for] the [other] people [MTY] in Israel and Judah, I will be [like] [MET] a stone that causes people to stumble, a rock that causes them to fall down. [And as for] the people of Jerusalem, I will be [like] [MET] a trap or a snare [DOU].
zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
15 Many [people] will stumble and fall down and never get up again. They will experience great troubles; they will be captured [by their enemies].”
Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
16 [So, I say to you who are my disciples], seal up this scroll on which I have written the messages that God has given to me, and give his instructions to [others] who have accompanied me.
Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
17 I will wait to see what Yahweh [will do]. He has rejected the descendants [MTY] of Jacob, but I will confidently expect him to help me.
Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
18 I and the children that Yahweh has given to me are [like] signs to warn [the people of] Israel; we are warnings from the Commander of the armies of angels the one who lives [in his temple] on Zion Hill [in Jerusalem].
Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
19 Some people may urge you(pl) to (consult/go and talk with) those who talk with the spirits of dead people or with those who say that they receive messages from those spirits. They whisper and mutter [about what we should do in the future]. But God is [RHQ] the one whom we should ask to guide us! It is ridiculous [RHQ] for people who are alive to request spirits of dead people to tell us [what we should do]!
Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
20 Pay attention to God’s instructions and teaching! If people do not say things that agree with what God teaches us, [what they say is worthless]. [It is as though] those people are in darkness.
Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
21 They will wander through the land, worried/discouraged and hungry. And when they become [very] hungry, they will become very angry. They will look up [toward heaven] and curse God and [will also] curse their king.
Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
22 They will look around the land and see only trouble/distress and darkness and things that cause them to despair. And [then] they will be thrown into the very black darkness [of hell]. (questioned)
Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.

< Isaiah 8 >