< Isaiah 57 >
1 Righteous people [sometimes] die [when they are still young], and no one is concerned about it. Godly people [sometimes] die because of disasters, and no one understands why. They are taken away in order that they will not endure more calamities,
Mai adalci yakan mutu, ba kuwa wanda yakan yi tunani a zuciyarsa; an kwashe mutanen kirki, ba kuwa wanda ya fahimta cewa an kwashe masu adalci don a tsame su daga mugunta.
2 and now they have peace. They [continually] lived righteously, and [now] they rest [peacefully] in their graves.
Waɗanda suke aikata abin da yake daidai sukan shiga da salama; sukan huta yayinda suka kwanta cikin kabari.
3 [Yahweh says, ] “But you who practice sorcery, come here! You who worship idols [MET], [listen to me]!
“Amma ku, ku matso nan, ku’ya’ya maza na masu sihiri, ku zuriyar mazinata da karuwai!
4 Do you realize [RHQ] whom you are ridiculing, and whom you are insulting? Do you realize [RHQ] to whom you are sticking out your tongues? [You are insulting me, Yahweh]! You are [RHQ] always rebelling against me and always lying.
Wane ne kuke yi wa ba’a? Ga wa kuke masa gwalo kuna kuma fitar da harshe? Ashe, ku ba tarin’yan tawaye ba ne, zuriyar maƙaryata?
5 You are eager to have sex under every [big] green tree where you worship your gods. You kill your children as sacrifices [to your idols] in the dry riverbeds, and [also] offer them [as sacrifices to your idols] in the rocky caves.
Kuna cike da muguwar sha’awa mai ƙonawa a cikin itatuwan oak da kuma a ƙarƙashin kowane itace mai inuwa; kuna miƙa hadayar’ya’yanku a rafuffuka da kuma a ƙarƙashin tsagaggun duwatsu.
6 [You take big] smooth stones from the riverbeds and worship them as your gods. You pour out [wine] to be an offering to them, and you bring grain [to burn for] an offering to them. Do you think that I should not punish you for doing all those things?
Gumakan da suke cikin duwatsu masu sulɓi su ne rabonku; su ɗin, su ne rabonku. I, gare su kuka kwarara hadayu na sha kuka kuma miƙa hadayu na gari. Saboda waɗannan abubuwa, zan yi haƙuri?
7 You have sex [EUP] [with cult prostitutes] on every hill and mountain, and you go there to offer sacrifices [to your gods].
Kun yi gadonku a dogayen duwatsu masu tsayi da kuma a tudu mai tsawo; a can kuka haura don ku miƙa hadayunku.
8 You have put (fetishes/pagan symbols) behind your doors and doorposts, and you have deserted me. You have taken off your clothes [EUP] and climbed into your bed and invited more [of your lovers] to come to bed with you. You have paid them to have sex with you, and you have fondled their sexual organs.
A bayan ƙofofi da madogaran ƙofofi kuka kafa alamun gumakanku. Kuka yashe ni, kuka kware gadonku, kuka kwanta a kansa kuka fadada shi; kuka kuma ƙulla yarjejjeniya da waɗanda kuke ƙaunar gadajensu, kuka dubi tsiraicinsu.
9 You have given [fragrant] oil and lots of perfume to your god Molech, and you sent messengers to distant countries [to find other gods to worship]; you [even tried to] send [messengers] to the place of the dead [to search for new gods]. (Sheol )
Kuka tafi wurin Molek da man zaitun kuka kuma riɓaɓɓanya turarenku. Kuka aika jakadunku can da nisa; kuka gangara zuwa cikin kabari kansa! (Sheol )
10 You became weary because of doing all those things, but you never said, ‘It is useless [for us to do that].’ You found new strength for worshiping idols, so you continued to do that [LIT].
Kuka gaji cikin dukan al’amuranku, amma ba ku iya cewa, ‘Aikin banza ne ba.’ Kuka sami sabuntar ƙarfinku, ta haka ba ku suma ba.
11 Was it because you were afraid [of those idols more than you were afraid of me] that you lied [about what you were doing], and you do not even think about [DOU, RHQ] me? Was it because I did not punish you for a long time that you are not afraid of me [RHQ]?
“Wa ya sa ku fargaba, kuna jin tsoro har kuka yi mini ƙarya, ba ku kuma tuna da ni ba balle ku yi tunanin wannan a zukatanku? Ba don na daɗe ina shiru ba ne ya sa ba kwa tsorona?
12 You [think that] [IRO] the things that you have done are right, but I will tell the truth. It will not help you to do any of those things.
Zan bayyana adalcinku da kuma ayyukanku, ba kuwa za su amfane ku ba.
13 When you cry out [for help] to your collection of idols, they will not rescue you. The wind will blow them away [DOU]. But those who trust in me will live in the land [of Israel], and [they will worship me on Zion], my sacred hill.”
Sa’ad da kuka nemi taimako, bari tarin gumakanku su cece ku! Iska za tă kwashe dukansu tă tafi, ɗan numfashi kawai zai hura su. Amma mutumin da ya mai da ni mafakarsa zai gāji ƙasar ya kuma mallaki dutsena mai tsarki.”
14 Yahweh will say, “Prepare [yourselves to receive] me, [like] [MET] people build and prepare a road [for a king to come on]. Get rid of [the things that are causing you to sin] [like] [MET] people remove from a road (obstacles/things that cause people to stumble).
Za a kuma ce, “Ku gina, ku gina, ku gyara hanya! Ku kawar da abubuwan sa tuntuɓe a hanyar mutanena.”
15 Because this is what [I], Yahweh, who am holy and greatly honored and who live forever, say: I live in the highest heaven, where [everything] is holy, but I also am with those who are humble and who are sorry for the sinful things that they have done. I will greatly encourage [DOU] those who have repented.
Gama abin da Maɗaukaki da kuma Mai daraja ya faɗa wanda yake raye har abada, wanda sunansa mai tsarki ne, “Ina zama a bisa da kuma a tsattsarkan wuri, amma kuma tare da shi wanda yake mai halin tuba mai tawali’u a ruhu, don in farfaɗo da ruhu mai tawali’u in kuma farfaɗo da zuciyar mai halin tuba.
16 I will not accuse [people] forever; I will not always be angry [with them], because [if I did that], people would become weak/discouraged; all the people whom I created and caused to live would die.
Ba zan tuhume su har abada ba, ba kuwa kullum zai yi fushi ba, gama a haka ruhun mutumin zan yi suma a gabana, shi numfashin mutumin da na halitta.
17 I was angry [with my people] because they sinned by wanting the things that others had. So because I was angry, I punished them and turned away from them, but they continued sinning.
Na yi fushi saboda kwaɗayin zunubinsa; na yi masa horo, na kuma ɓoye fuskata saboda fushi, duk da haka ya ci gaba da ayyukan zunubinsa.
18 I have seen the evil things that they continually do, but I will restore them and lead them. I will encourage/comfort them. And to those who are mourning,
Na ga al’amuransa, amma zan warkar da shi; zan bi da shi in mayar da ta’aziyya a gare shi,
19 I will enable them to sing songs to praise me. I will restore [all my people], those who live near [Jerusalem] and those who live far away, and I will cause things to go well for them.
ina ƙirƙiro yabo a leɓunan masu makoki a Isra’ila. Salama, salama, ga waɗanda suke nesa da kuma kusa,” in ji Ubangiji. “Zan kuma warkar da su.”
20 Wicked [people do not have peace in their inner beings]; they are like [SIM] a sea [whose waves are] always churning up mud,
Amma mugaye suna kama da tumbatsar teku, wanda ba ya natsuwa, wanda raƙumansa sukan kawo gurɓacewa da tabo.
21 and [I], Yahweh, say that things will never (go well/be peaceful) for those who are evil.”
“Babu salama ga mugaye,” in ji Allahna.