< Isaiah 55 >

1 “All you [people who are in exile], listen to me! [It is as though] [MET] you are thirsty, so come and get water from me! [It is as though] you have no money, but you can come and get things from me [that are like] wine and milk! You can get [what you need from me], [and] you will not need to give me any money for them!
“Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
2 [What you really need is to have a close relationship with me], so (why do you spend money to buy things that do not supply what you really need?/you should not spend money to buy things that do not supply what you really need.) [RHQ] (Why do you work hard to get money to buy things that do not (satisfy your [inner beings]/cause you to be happy)?) [RHQ] Pay attention to what I say and acquire what is really good [MET]! If you do that, then you will truly be happy [MET].
Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
3 Listen to me and come to me; pay attention to me, and if you do that, you will have new life in your souls. I will make an agreement with you that will last forever to faithfully love you like I loved [King] David.
Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
4 By what he did, I showed [my power to many] people-groups; I caused him to be a leader and commander [DOU] over [the people of many nations].
Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
5 And similarly, you will summon people of other nations to come to you, nations that previously you have not heard about, and they had not heard about you; and they will come to you quickly because [they will have heard that I], Yahweh, your God, the Holy One of Israel, have honored you.
Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
6 Seek [to know] me while it is still possible for you to do that; call to me while I am near!
Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
7 Wicked [people] should abandon their wicked behavior, and evil people should stop thinking what is evil. They should turn to me, and if they do that, I will act mercifully toward them; they should turn to me, their God, because I will fully pardon them [for all the wicked things that they have done].
Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
8 I, Yahweh, declare that what I think is not the same as what you think, and what I do is very different from what you do.
“Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
9 Just as the sky is far above the earth, what I do is far greater than what you do, and what I think is much greater than what you think.
“Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
10 Rain and snow come down from the sky, and they cause the ground to be moist before the moisture returns [to the sky and produces more clouds]. When the ground becomes moist, it causes plants to sprout and grow, with the result that the soil produces seed for the farmer [to plant] and [grain to produce flour to make] bread for people to eat.
Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
11 And similarly the things that I promise to do, I will [always] cause to happen; my promises will [always] be fulfilled [LIT]. They will accomplish the things that I gave them to accomplish [DOU].
haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
12 You will leave [Babylon] joyfully, you will have peace as I lead you out. [It will be as though] the hills and mountains will sing joyfully, and the trees in the fields will clap their hands.
Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
13 Instead of thornbushes and briers, pine/cypress [trees] and myrtle [trees] will grow [in your land]. As a result of that, people will honor me much more; and what I do will remind everyone that [I do what I have promised].”
A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”

< Isaiah 55 >