< Isaiah 41 >

1 [Yahweh says], “You [people who live on] [APO] islands in the ocean, be silent in front of me [while I ask you some questions]! Then you can be courageous and talk to me. We will meet together and decide [which one of us is right].
“Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
2 Who has urged this king to come from the east? Who has enabled his [army] to righteously defeat many nations and to trample their kings under their feet? With their swords they cut [their enemies] into tiny pieces [HYP]; with their arrows they cause their enemies to scatter like [SIM] the wind scatters chaff.
“Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
3 Even though they march through areas where they have not gone previously, they pursue [their enemies] and continue to march, and nothing stops them.
Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
4 Who has enabled rulers to do [DOU] mighty things like that? Who has done that throughout all generations? It is I, Yahweh; I was the first [one to do things like that], and I will be the last one [to do them].”
Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
5 [People who live on] [PRS] islands in the ocean are afraid while they watch. People in remote areas tremble and gather together.
Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
6 They encourage each other and say to each other, “Be strong!'
kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
7 The craftsmen encourage those who make things from gold, and the men who flatten metal encourage those who hammer metal (on an anvil/into shape). They all say, “The idol has been well made!” And then they carefully nail down the idol in order that it will not topple over!
Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
8 [Yahweh says], “[You people of] Israel [are like] my servants; you are [descendants of] Jacob, whom I chose; [you are] descendants of Abraham, who [I said is] my friend.
“Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
9 I summoned you from very distant places [DOU] on the earth, and I said ‘I [want you to] serve me; I have chosen you, and I will not reject you.’
na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
10 Do not be afraid, because I will (be with/help) you. Do not be discouraged, because I am your God. I will enable you to be strong, and I will help you; I will hold you up with my powerful arm by which you will be rescued.
Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
11 It is certain that all those who are angry with you [Israeli people] will be disgraced [DOU]. Those who oppose you will be wiped out; they will all die.
“Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
12 If you search for those who tried to conquer you, you will not find them, [because they will all have disappeared]. Those who attacked you will not exist [any more].
Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
13 [It will be as though] I will hold you up by your right hand. I am Yahweh, your God, and I say to you, ‘Do not be afraid, [because] I will help you.’
Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
14 Although you people of Israel [DOU] [think that you are as insignificant as] worms, do not be afraid [of your enemies], because I will help you. I am Yahweh, the one who rescues you; I am the Holy One of Israel.
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
15 [I will cause] you to be like [MET] a (threshing sledge/big piece of metal that has sharp teeth for separating grain from chaff). You will tear [your enemies to bits], causing them to be like bits of chaff on the mountains.
“Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
16 You will toss them up into the air, and a strong wind will blow them away [DOU]. [When that happens], you will rejoice about what I [have done for you]; you will praise me, the Holy One of Israel.
Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
17 When poor and needy people need water and they have no water, and their tongues are very dry because they are very thirsty, I, Yahweh, will come and help them. I, the God to whom you Israeli people belong, will never abandon them.
“Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
18 I will cause rivers to flow for them on the barren hills. I will give them fountains in the valleys. I will fill [HYP] the desert with pools of water. Water from springs will flow into rivers, and the rivers will flow across the dry ground.
Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
19 I will plant [trees] in the desert— cedar [trees], acacia [trees], myrtle [trees], olive [trees], cypress [trees], fir [trees], and pine [trees].
Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
20 [I will do that] in order that people who see it will think about it, and they will know and understand [DOU] that it is [I], Yahweh, who have done it; it is what [I], the Holy One of Israel, have done.
don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
21 [I], Yahweh, the true king of Israel say [to you nations], “Tell what your idols can do for you!
“Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
22 Bring them here to tell us what is going to happen! Ask them to tell us what things happened long ago, in order that we may think about those things, and learn if those things that they predicted really happened. Or, ask them to tell us about the future, in order that we can know what will happen.
“Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
23 [Yes], those idols should tell us what will happen in the future. If they do that, we will know that they are really gods. Tell them to do something—either something good or something bad! Tell them to do something that will cause us to be amazed and afraid!
faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
24 But [that is impossible, because] idols are absolutely worthless [HYP]; they can do nothing, and I detest those who decide [to worship] idols.”
Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
25 “[But] I have incited/urged a ruler who will come [with his army] from the north. I have summoned him to come from [his country, which is] east [of Israel], and I have given him my authority [MTY]. I will [enable his army to conquer other rulers]; they will trample those leaders like [SIM] a man who makes clay pots first tramples the clay.
“Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
26 (Who told you people long ago that this would happen?/No one told you people long ago that this would happen!) [RHQ] (Who predicted it, with the result that we can say, ‘What he predicted was correct!’?/No one predicted it, with the result that we can say, ‘What he predicted was correct!’) [RHQ] No one else said that it would happen.
Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
27 I was the first one to tell [the people of] Jerusalem, ‘Listen to this! I have appointed a messenger to tell good news to you!’
Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
28 None of your idols told you that [DOU]. And when I asked them questions, none of them was able to give me any answers.
Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
29 Think about it: Those idols are all useless, worthless [DOU] things. They are [as meaningless as] [MET] the wind.”
Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.

< Isaiah 41 >